3

809 58 0
                                    

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA


PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

SADAUKARWA GA ƘUNGIYAR PERFECT WRITERS ASSOCIATION, DOMIN TAYA MURNAR CIKA SHEKARU BIYU DA KAFUWA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.


Page3




Tana zuwa unguwar su ta sauka, ta biya me napep kuɗi, ta shige gida kanta tsaye, seda ta shiga ma ta fara tunanin tijarar da zata sha yau, kwana biyar bata gida, dakewa tayi kanta tsaye ta shige, da sallama ta shiga abunta lokacin ana ta kiraye Kirayen sallar magariba, ta tarar ba kowa a tsakar gidan se Babarsu Sadiya tana iza wutar girki.

Ta ɗago ta kalli Amira tace 'ke daga ina? Kwana biyar Amira Babu wanda yasan inda kike? Yanzu kinwa kanki adalci kenan?"

Tsaki Amira tayi ta shige ɗakinsu, ta tarar da Sadiya da Amina suna salla, ta ajiye mayafinta taje tayo alwala ta tada salla, bayan ta idar tana lazimi tana jin yadda su Sadiya keyi da ita.

Amina tace "hmm lalacewa ta ƙaru, likkafa ta cigaba, su O'o yanzu har kwana ake a waje"

Sadiya tace "kwanaki dai, yau kwananta nawa bata gidan nan, ni azo a gayawa Baba gaskiya a raba mana ɗaki da ita, baze yuwu ba, kar muje mu kwashi cuta wallahi"

Banza Amira tayi musu, ta ƙarasa laziminta, tana tunanin abunda zata fuskanta idan Baba ya dawo.

Tana cikin wannan tunanin ne akayi Sallama da Sadiya, saurayinta yazo ta tashi ta fita.

Baba ne yai Sallama ya shigo shida Usman, sun dawo daga masallaci, suna shigowa Maman su Sadiya ta fara kora bayani.

"Baba, se yau Allah yayi wannan mara albarkar ta dawo, kwana biyar cif bata gidan nan, Babu wanda yasan inda take kwata kwata, kaga alamu sun bayyana ƙarara tafi ƙarfin kowa yanzu, Babu alamar nadama a tare da ita balle asa ran tuba"

Baba yace "ni nama rasa abun faɗa akan wannan yarinyar wallahi, har kunyar shiga cikin mutane nake, saboda abunda take aikatawa"

Wata matar ce ta fito daga wani ɗaki tace "Ai Malam dole a san abunyi, tun bata kwaso mana abun kunya ba, ko ta kwaso wata cutar taje ta gama mana a gida ba"

Maman Sadiya tace "kokuma ta hana yaranmu auruwa ba, tunda gidansu ɗaya kar ace duk halinsu ɗaya"

Saboda tsabar ƙarfin hali irin na Amira, bata nuna tasan da ita suke bama, ta fito abunta zata wuce gurin da ake girki.

Tsawa Usman yai mata yace "Ke! Gidan ubanwa kika tafi tsawon wannan lokacin?"

"Gidan Uban mutum" ta bashi amsa

Amira ta bashi amsar cikin natsuwa.

"Ni kike zagi?' yai maganar yana nunata da yatsa.

"Kai ka ɗaine Mutum a gurin nan? Bana son kalen jaraba fa tom, ban kula kowa ba dan haka a sauraramin"

WUTA A MASAƘAWhere stories live. Discover now