WUTA A MASAƘA 29_30

750 48 3
                                    

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

The experience writer of

*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.

29_30



Bayan fitar Imran, Ihsan ta rasa abunda yake mata daɗi, gaba ɗaya ta rasa meke mata daɗi, shigowar Amira rayuwarsu babbar barazana ce ga farin cikinta, gaba ɗaya taji ta tsani Amira wani mugun haushinta take ji.

Ɓangaren Amira ma tunani kawai take akan irin zaman da zatayi a gidan Imran, dan ta ƙudirce a ranta ba zata juri wulaƙanci ba ko kaɗan.

Ihsan seda ta wuni cir Imran be dawo gida ba, dan se bayan tara n dare sannan ya dawo Gidan, da ya dawo ɗin ma be bi ta kanta ba, ya nemi guri yai kwanciyar sa ya bi lafiyar gado abunsa.

Mamaki ya cika Ihsan, ita da akaiwa Laifi amma shine yake fushi, yai watsi da Ita, gani tayi Imran ba shi da niyyar saurararta.

Har wayewar gari ya shirya yai ficewar sa gurin aiki, koda wasa bata taɓa kawo akwai abunda ze kawo mata tangarɗa a rayuwar auren da suka tsara yi ita da Imran ba, se gashi katsam Amira ta kutso rayuwarsu.

Ihsan gaba daya ta shiga damuwa da tunanin idan Amira ta shigo gidan wani irin zama zasuyi, dan yau da gobe se Allah, Amira ta cika macen da zata wuce a kalla, tai shiru tana tunanin ina mafita.

Se magariba sannan Imran ya dawo, kuma ba wannan ne lokacin da ya saba dawowa ba, ta tashi ta karɓi ƙatuwar jakarsa ta sojoji, be kulata ba ya wuce ɗaki abunsa, yai wanka ya fita sallar magariba, be dawo ba se isha'i, bayan ya dawo yace "My a kawo Abinci ne?"

"No karki damu naci Abinci"

"Haba my D ban cancanci haka daga gareka ba, kana nufin kar inyi kishi akanka kenan? Wani kalar zama zamuyi kuma ranar da ta tare? Akwai yiwuwar ka juyamin baya kenan?"

"Ihsan ba haka bane, na rasa ya ki ke son inyi ne, na miki bayani amma kin kasa ganewa, kishi yana rufe miki ido da yawa, kin kasa fahimta ta gaba ɗaya, ni ba wani abu tsakani na da Yarinyar nan, na gaya miki komai da yadda aka yi na Aure ta, amma kin kasa fahimta, ta yaya zata gaya miki magana ki yadda, baki san halin yarinyar nan bane, idan har ki kace zaki biye abun da zata dinga faɗa, to tabbas za mu dinga samun saɓani, ni ba burina bane in dinga ɓata miki rai ba, ina sonki Ihsan meze sa in muzguna miki? Amma kishi yana rufe miki ido da yawa Why Ihsan?"

"Kayi haƙuri Please, ba zan sake ba insha Allah"

"Yawwa ko ke fa my deari, I miss you fa"

Yai maganar yana rungumeta, tare da faɗaɗa murmushinsa, da haka suka shirya suka sake jefa babin Amira a kwandon shara.

Amira kam ita kanta ta san fatar jikinta tayi kyau, kamar bata shiga rana, ta ƙara ƙiba hutawa kawai take, kusan kullum tana tare da Fadila, tana koyon girke girken 'yan gayu wanda bata iya ba, sam Amira ba ta da ƙyuya, Akwai gyara bata son ƙazanta kwata kwata.

WUTA A MASAƘAWhere stories live. Discover now