35_36

854 51 4
                                    

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

The experience writer of

*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.

35_36




Saroro Imran yai yana kallon Amira, da tuni idanunta su kai ja, ta juya ta koma part ɗinta zuciyarta na wani Mugun tafasa.

Duk da jifan sa da Amira tayi da bokiti, ko gezau be ba haka bokitin ya daki ƙirjinsa da ƙarfi ya faɗi.

Ihsan zuba ido tai ta ga Iya abun da Imran ze, ta ga matakin da ze ɗauka akan Amira, amma taga kawai yai waje ba tare da yace komai ba ko ya ɗau wani mataki ba.

Mamaki ne ya cika Ihsan, wai kenan Amira taci bulus? Me Imran yake nufi da ƙyale Amira ba tare da wani hukunci ba? Ta masa wannan fitsarar har da duka amma ya gaza ɗaukar mataki?

Amira kam seda tai ƙaramin hauka a ɗaki ita kaɗai, gaba ɗaya ta fita hayyacinta saboda kuka, ta zama kamar wata wadda ta daɗe ta na cuta, idanunta suka kumbura su kai jawur saboda kuka.

Haka tai me isar ta ta haƙura, ko Abincin rana kasa ci tayi saboda yadda take jin zuciyarta.

Imran kuwa bayan fitarsa Khalid ya kira shi a waya, kamar ya share kiran kar ya ɗaga, seda ta kusa katsewa sannan ya ɗaga.

"Malam wai baka kusa da wayar ne da se da ta kusa katsewa sannan zaka ɗauka, ko duk matan ne suka ɗauke maka hankali?".

"Ƙyaleni kawai Khalid, suna neman su maida ni mahaukaci ne kawai".

"Mahaukaci kamar Yaya?"

"Wai dama haka Auren mata da yawa yake? Kullum cikin faɗa da tashin hankali, yau ni Amira ta jefawa bokiti a ƙirji, ni nama rasa me zanyi, dan idan nace zan dake ta rainani zata yi kawai, kuma zan iyayi mata illa, dan duka zan mata na gaske"

Khalid yace "Subhanallah, wai haryanzu Amira ba tai hankali ba kake nufi?"

"Ina Wannan yarinyar za tai hankali, kullum cikin faɗa kamar dage, ba afuwa a lamarinta kullum cikin neman rigima".

"A'a Imran, haka kurum ba zata nemi rigima ba, me a kai mata ta nemi rigima, ka dinga mata adalci fa"

"Kaga dan Allah ƙyaleni, karka ƙara tunzurani, dan tunanin hukuncin da zan mata nake"

"Wane hukunci, ai tunda ba ka hukunta ta a lokacin ba kawai ka manta, kayi haƙuri ya wuce kawai".

"Saboda rashin mutunci, ta min laifi kuma in ƙyaleta?".

"Kai me kai mata tai maka hakan?"

Tsaki Imran yai yace "ka ga, kiran me kayi min ne?"

"Dama kira nayi inji lafiyar ka, sannan ka kalli News ɗazu da safe kuwa?"

WUTA A MASAƘAWhere stories live. Discover now