37_38

851 54 4
                                    

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

The experience writer of

*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.

37_38

Sake fashewa da kuka Amira tayi tace "ni dai ba na son ka tafi"

Ɗan shiru yai yana kallonta "meyasa ba kya so na tafi?"

"Ana kashe mutane, kuma bana so a kashe ka"

Jikin Imran yai sanyi sosai, ya kalli yadda ta riƙe hannunsa, ga idanunta na zubda hawaye.

Gyara tsayuwarsa yai, ya ɗago fuskarta, ta na kallonsa, fuskarta duk cizon sauro ga idanunta sunyi jawur"

A hankali yace "kin kwana a falo sauro ya cije ki, kinga zazzaɓi ya rufeki, kije ki kwanta zuwa anjima ki kira Anty a waya, a kawo miki magani, zan tafi abokan tafiya ta suna jirana, dan Allah ban da faɗa ko tashin hankali, ni na tafi"

Ya zame hannunsa a hankali, ya juya ya fara tafiya, bayansa ta bi da kallo, har ya fita daga falon.

Jiki a sanyaye ta koma ta Kitchen, ta leƙa window, ta ga sojoji a harabar gidan jikinsu da Uniform, suka hau mota suka fita.

Amira ta zauna a Kitchen ɗin ta haɗa kai da gwiwa tana maimaita 'Innalillahi wa inna ilaihi raji'un"

Sun yi nisa a tafiyar, Imran ya kira Anty, tana tsaka da aiki ta ga kiran nasa, amma tai ƙoƙari ta ɗaga wayar "Anty barka da safiya"

"Yawwa barka Imran, ya kake ya gida?"

"Lafiya ƙalau, ya aiki?"

"Aiki Alhamdilillah, mun fito tun ɗazu"

"Masha Allah, dama Anty nace dan Allah idan ban takura ki ba, kinga an turani aiki Zamfara ne, kuma na bar Amira ba lafiya, ban san lokacin da zan dawo ba, nace in ba damuwa ko zata zauna a gurinki, kan inga yadda Allah zeyi damu, tunda babu me kula da ita a gidan"

Anty tace "Ni da 'yata amma ka dinga cewa in ba zaka takuramin ba, ai gara da ka gayamin inje in ɗakko abata, yanzu Zamafaran aka turaku Imran?"

"Wallahi kuwa Anty, kin ganmu a hanya ma"

"Subhanallah, to Ubangiji Allah ya tsare mana ku, ya kaiku lafiya ya dawo da ku lafiya, Amirana kuma Allah yasa rabo muka samu"

Imran yace "Rabon me kuma Anty?'

"Rabon Baby mana, zan ɗau jika"

"Hmmm Anty kenan, ai mana addu'a dawowa lafiya"

"Insha Allah zamuyi, Allah ya tsare"

"Ameen Anty nagode"

Ya katse wayar.

Duk da yasan Ammi tana jin haushin sa amma ya kirata a waya, suka gaisa ta amsa masa sama sama, yace "Ammi ina buƙatar addu'rki, ina hanyar Zamfara ne"

WUTA A MASAƘAWhere stories live. Discover now