UKU-BALA'I=20

716 35 0
                                    

UKU-BALA'I

NA

KAMALA MINNA

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.

BABI NA ASHIRIN.

Dubansa take yi da wani irin yanayi na na raina wayonka da azanicin ka kafun ta kau da kai tana mai sakin guntun tsaki ta nisa cikin yanayi na haushi.

"Ban san mai ya hau kan ba Dr.Erena sosai ka bani mamaki ban taba zaton kalaman nan za su iya fitowa ɗaga bakin ka ba ka dube ni up zuwa down ban yi maka kama da mai karamin tunani irin naka ba aiki na zo yi a wannan company ba zaman zance mara kan gado ba".

Ta karashe tana mikewa kan kafafuwanta fuskar dauke da tsananin bacin rai sai dai kuma acan kasar ruhinta da zuciyarta ba haka bane domin kuwa murna take har da tsalle-tsalle Dr.Erena ya kusan fadowa komarta abin da ta jima tana KUDIRI da muradin tabbatarsa kenan.

"Areef..".

Da sauri ta daga masa hannu kafun ta dauki jakarta dake ajje kan table din Office din nasa.

"Ya isa haka bana bukata ban so ka takura min, in kuma kace takura min zakayi wallahi yanzun nan zan rubuta maka takardar ajje aiki...".

Da sauri ya mike jin abin da take fadi jikinsa har ɓari yake yi ya iso inda take tsaye ya kafeta da idanunsa da suka gama tafiya a duniyar Areefa.

"No Please ba sai mun je wannan matakin ba...But Areefa ya kamata ki fahimce ni mana  alkawari nayi miki komai kike so kuma ko me kike so ayi na miki alkawari...".

Da sauri ta watsa masa wani kallo wanda yake kara rikita masa lissafi kafun ta tsume fuska.

"Ban san ta ya  zan maka bayani ka fuskanta ba Dr.Erena ban san da wani irin kalami zan yi amfani ka gane abin da nake nufi ba".

Tana gama fadin haka ta fara taka kafafun ta ta doshi kofar fita zuciyarta cike da abubuwa masu matukar yawa.

Shi kuwa shanye baki yayi yana kallonta har ta fice kafun ya ajje wani numfashi mai karfi ya koma ya zube kan daya daga kujerun Office din nasa.

******

First Class International School Gwada.

Sosai farinciki ke wanzuwa a fuskarta tun lokacin da Dr.Karami ya danko ta  daga gida zuwa haɗaɗɗiyar makarantar da ya zaba mata zata cigaba da karatun ta.

Zaune take zuciyarta falla da farinciki mara musaltuwa har da guntayen hawayen na farinciki duban Dr.Karami take cikin wani irin yanayi wanda ita kanta ta kasa tantacce matsayin da take ji ya samu a zuciyarta sosai take jin matsayi mai girma game dashi a filin zuciyarta sosai take jin komai na canzawa a duniyar rayuwarta a yau daya kadai sosai take hango mafarkinta zai tabbata na son karatu da ta jima tana rokon Allah ya bata damar da za tayi shi yau gashi Allah ya jeho mata Dr.Ƙarami mutumin da bata taba zaton za ta gan shi a duniyar mafarkin ta ba balle a zahiri amma gashi Allah ya kawo matashi ta hanyar da bata yi zato ko tsammani ba.

Numfashi ta ja kafun ta dago kai ta na kallon Office din da ta baro shi a ciki shi da shugaban makarantar suna zantawa.

Kamar daga sama taji an dafa mata kafaɗa da sauri ta dawo daga duniyar tunanin da ta fada dago kanta tayi ta sauke kan wata matashiyar yarinya wacce a shekaru za suyi kai daya sai faman murmushi take sakar mata cikin yake ita ma Mariya ta sakar mata da martani.

"Sannu ko sunana Baseera Haruna Sa'eed ni sabuwar daliba ce da Dadyna ya kawoni yau ke ya sunanki".

Mariya da ta saki baki da idanuwa ta na kallon ikon Allah sai yanzu ta kyafta idanu kafun ta sake murmushi tana motsa laɓɓanta cikin mamaki da wannan kanzagi da zalaka na wannan yarinyar sai kace ta tambaye ta saki baki sai ratata zance take yi kamar an kunna rediyo ana sauraron shirin INDA RANKA.

UKU BALA'I (Completed)Where stories live. Discover now