17 Shi Ne Ko Ba Shi Ba Ne?

2.2K 213 11
                                    

*🅰MRAH NAKE SO!* ♥

(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)

Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_

1⃣7⃣

Tun daga lokacin da soyayya mai 'karfi ta gama shiga tsakaninsu, zuciyata take ciki da farin ciki.

Sosai ciwonta ya yi sauk'i kuma, tun daga sanda suka dawo daga Saudiyya, har yanzu.

Yanzu haka Amrah ta shiga SS2 ne har ma sun kusa shiga 3, Annur kuma ya samu aiki a wani babban kamfanin k'ere-k'eren motoci da ke Birnin Abuja, yana masu aiki ta b'angaren zane-zane.

Hajiya Suhaila kuma ta samu Dady'n su Noor da maganarsa shi da Amrah, bai hana ba, saboda shi dama babban burinsa dai yaransa su ginu bisa tafarki mai kyau, su samu ingantaccen ilimi wanda zasu amfana da shi, kuma ya yi alfahari da su. Kuma Noor d'insa ya samu. Dan haka ba zai hana sa auren duk wacce ransa ke so ba.

A lokacin da ta shiga SS 3 ne aka fara maganar aure, har ma manya sun shiga maganar.

Har a tsawon wannan lokacin Amrah bata daina tunanin mutumin da ta yawaita gani a asibiti cikin keken guragu ba, bata daina mamakin mutumin ba, sau da dama ta kan same ni da maganar,

"Umma na rasa yanda zan yi na cire wancan mutumin daga zuciyata. A duk sanda zan zauna ni ka'dai, ya kan fad'o min a rai. Na rasa ko shi d'in waye, ban tab'a ganin kama irin tasu ba."

"Ba abun tunani ba ne wannan ba Amrah. Kin san a duniyar nan ana kama, akwai wanda kai kanka idan ka kalle shi zaka san kuna kama, kuma a zahirin gaskiya baka had'a komai da shi ba. Dan haka ki daina wannan tunanin. Annur d'inki dai shi ne kawai, kuma insha Allahu shi zaki aura."

Da kunya ta duk'ar da kanta k'asa, tana wasa da yatsun hannunta.

Kud'in neman auren Amrah kansu dubu d'ari biyu aka kawo, a raina har ina jin kamar sun yi yawa.

Haka kayan saka rana da aka kawo, komai a wadace, katan katan d'in abubuwa haka aka ringa dire su a tsakar gidanmu.

Wata bakwai aka saka auren, wanda ya yi dai-dai da gama makarantarta.

Daga sanda aka kawo kayan saka rana, kafin a raba su sai da ta yi saukar Al-Qur'ani, tana fatan Allah Ya saka albarka a rayuwar da zata tsinci kanta, rayuwar da take yawan tunanin fad'amawa, take jin ina ma a ce a gidansu zata yita zama ko bayan auren. Ko kad'an bata son abin da zai raba ta da gida. Duk sanda zan yi wata tafiya zuwa garinmu, kafin in dawo sai ta yi ciwo, ba wai ciwon sikilarta ba, ciwon rashi na a kusa da ita kawai. Saudiya ma da ta je ashe daga farko sai da ta yi, daga baya ne ta koma dai-dai. To bare kuma yanzu da zata tafi ta bar ni, bari na har abada. Zata fad'a wata sabuwar rayuwar, mai cike da k'alubale.

Ba wai Amrah kad'ai ba, ni ma kaina da na haife ta dan dai aure ya zama dole ne. Har ji nake a raina 'Banda aure ibada ne, me zai sa ka haifi 'yarka, ka raine ta tun tana 'karama, ka so ta, ta so ka, amma rana d'aya wani ya raba ka da ita?'

Hawaye nake ni kad'ai a duk sanda na keb'e, nake irin wannan tunanin.

Ya zan yi da tunanin Amrah bayan barinta gida? Ya zan yi na cire tunaninta daga zuciyata? Wane hali zata ringa shiga a duk lokacin da ciwonta ya taso?

Sauk'in ma d'aya, bani da haufi ko kad'an a rayuwar da zata fad'a. Bana haufin wanda zata yi rayuwa a k'ark'ashinsa. Na tabbata zai kula da ita, tamkar yanda zan kula da ita. Zai nuna mata soyayya, fiye da yanda ni zan nuna mata. Zai bata ingantacciyar rayuwa, fiye da yanda ni zan bata.

AMRAH NAKE SO! (Completed✅)Where stories live. Discover now