54=UKU-BALA'I

316 26 11
                                    

Cikin hanzari ta fito daga cikin Toilet din jikinta daure da ta shawul  kallo daya zaka yi mata ka hango tsantsan tashin hankalin da take ciki

idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir kamar wacce tayi KUKAN DOLE kai kawo kawai take yi gabadaya kanta ya gama kullewa ta rasa me ya kamata tayi a yanzu wanda ya dace a daidai wannan lokaci amma ta rasa

gaɓadaya gaboɓin jikinta ji take yi kamar an lakaɗa mata duka ta ko ina.
Da hanzari ta isa bakin gadon dakin nata ta zauna tana mai da  numfashi kamar wacce tayi gudun fanfalaki wayarta da ke yashe gefe guda ta janyo tana mai dubanta tana

jujjuyawa har na tsayin dakiku kafun ta shiga latsata tana binciko lamba ta danna mata kira amma ina! Wayar akashe taji ta hakan ba karamin kara rikita mata kai yayi ba mikewa tayi da sauri ta nufi sif din dake dakin

buɗewa tayi ta janyo doguwa riga baƙa ta zurawa jikinta gami da yin rolling da mayafin ta janyo flatshoes ta sanya key din motarta da ke kan Mirrow ta dauka tare da dauko wayarta sai da ta karewa dakin kallo kafun ta fice cikin hanzari zuciyarta na kara tsinkewa da tashin hankali mai girman gaske.

Cikin hanzari ta fice zuwa tsakar gidan motarta kirar 406 mai launi ruwan toka ta shiga tare da yi mata key bayan ta buɗe get din gidan ta fice ziciyarta na kara rikicewa ba abin da take jiyowa sai sautin muryar Areefa da yarda take kuka tana ihu akan ta zo ta taimake ta zata mutu bata san mai za tayi mata ba ba ta san abin da ya kamata tayi a daidai wannan

lokacin ba tana tsoron Dr.Erena ya sake maimaita abin da ya zama shine sanadi a yanzu tana tsoron a sake komawa gidan jiya za tafi kowa bakinciki zata fi kowa takaici a duniyar nan domin komai ya faru da Areefa a yanzu da lokacin baya duk ita ce sila ta hanyarta komai ya ke tabbata.

Wasu hawaye ne ta ji sun sauko mata da sauri ta sanya hannu daya tana dauke su tana mai tuki jikinta a sanyaye zuciyarta ne ta shiga kai kawo tana so ta samo wanda zai taimaka mata da abin yi sosai kwanyarta take hayaki tana kokarin kamawa da wuta.

'Alhaji Abdulwahaab'

Sunan da ya zo mata kai kenan da sauri ta runtse idanunta kafun ta buɗe su tana jin wani irin yanayi a zuciyarta mai girma gaske da sauri ta gangara bakin titi tayi parking tana mai hada kanta da sitiyarin motar na dakiku sai faman sauke numfashi take kafun ta dago ta dubi wayarta

lambarsa ta binciko jikinta har rawa yake yi ta danna masa kira gami da karawa a kunne cikin kankanin lokaci ta shiga ruri amma ba a daga ba har ta katse sai da tayi haka sau uku a na hudu Allah ya taimaka ya dauka wani irin ajiyar numfashi tayi mai karfi tana mai cewa.

"Don Allah kana ina Alhaji Abdulwahaab akwai matsala fa sosai ina bukatar ka yanzu yanzun nan ko ina kake ina kan hanyar gidan Dr.Erena mu hadu acan".

Mamaki sosai ya cika shi jin abin da take fadi.

"Ban fahimce ki ba Hajiya Layla meke faruwa ne?".

Dafe kai tayi kafun ta sake nisawa.

"Ba mu da lokaci don Allah ka zo yanzun nan akwai matsala ce".

numfashi ya sauke cikin wani yanayi.

"Amma Hajiya Layla kin mata yanayin da muke ciki ne da Dr.Erena kin san za a samu matsala in har ya gane mu din ne muke tare da Areefa...".

UKU BALA'I (Completed)Where stories live. Discover now