The night

676 90 21
                                    

_The secret issues_
    *💖JYY💖*

*28-29*

*_Wattpad_*
https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb or Nimcyluv


*_Telegram_*  https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ

    '''About the Night'''

Not edited
  آللحمدالله
              ....Gudu suke har suka ƙarasa bakin ƙofar dasu an saki ƙara a cikinta,kansa ne ya sara da ƙarfi ya hakan ya bashi damar zubewa a wajan yay saurin dafe kansa tare da faɗin dukkan addu'ar da tazu bakinsa,yayinda ɓangare guda na zuciyarsa ya shiga beating very past hakan ya sanya ya ƙara durƙushewa a wajan tare da sakin wani wahalallan numfashi mai zafin gaske,ganin hakan ya sanya Sufyan sallake Fahad yay saurin faɗawa cikin ɗakin,abun mamakin tana ƙwance sambal a tsakin rayal bed ɗin idanunta na zubawar da hawaye yayinda ƙirjinta ke ɗagawa kamar zai fashe gida biyu,yadda take numfashi daɗan fisge² shi kaɗai zai tabbatar maka bata cikin nutsuwarta,duk da sanyin daɗin bai hana gumi zubu mata gaba ɗaya ta kiɗime ta fita hayyacinta,banda kanta da take fisgewa sai kuma bakinta dake rawa da alama tana son furta wani abu amma ta gagara,idan ka ɗauke waɗannan babu wani abu dake mutsi jikinta,ganin yadda take abu kamar zautacciya ya sanya shi hawa gadon tare da nufuwar inda take ƙwance.

Mama da take tsaye tana kallon Fahad tare da mamakin abinda ya samesa lkc ɗaya,cikin sanyin jiki ta ƙarasa wajansa tare da durƙusawa kusansa,kansa ta shafa tare da faɗin"Yarona mene yasa ka shiga wannan halin?"jikinta ya faɗa tare da ƙanƙameta gaba ɗaya jikinsa rawa yake jijiyuyin kansa su fitu sunyi raɗa² saman forehead ɗinsa,ganin kamar baya hayyacinsa yasa Mama fara tofa masa addu'a tare da bubbuga bayansa alamar rarrashi,ƙara matseta yay har sai data runtse idanunta,kansa ya ɗago ya zuba Mama tsumammun firgitattun idanunsa kansa ta shafa tace"Yarona"sharr wasu wahalallun siraran hawaye suka shiga zuba ta cikin idanunsa bakinsa na fara yace "Mamana zuciyata bugawa take ina jin zafi da raɗaɗi a heart ɗina tana beating tana tafiya da dukkan numfashi da tunanina haɗi da farin cikina"fuskarsa ta ƙara shafa jikin sanyin jiki tace"Yarona babu abinda yafi ƙarfin Ubangiji sai dai ba'a ruƙesa ba,ka miƙa lamarinka zuwa mahaliccinka tabbas sai shige maka gaba kuma zai zam gatanka,ka daina saka kanka cikin damuwa sbd bata magani,tabbas da ace damuwa nayin magani da tuni nima tayimin maganin abinda ke raina kayarda da ƙaddara ka ɗauki ta wakkali za kaji daɗi insha komai zai huce"numfashi ya sauke tare da lumshe idanunsa a ƙaro na biyu hawayen da yake ɓuyewa suka ƙara zubuwa daga cikin idanunsa,mai yasa ya bari rauninsa suka bayyana har haka?mai yasa ya kasa riƙe damuwar dake ransa?dole yay hankali ya shiga nutsuwarsa sbd lukutin yaƙine babba a gabansa idan har zai bari rauninsa ya bayyana mutane su fahimci damuwarsa,nauyayyiyar ajjiyar zuciya ya sauke a fili kuma ya fahimci Mama yace"tayaya zan samu sauƙi da sukuni a cikin zuciyata?tayaya damuwa zata bar zuciyata alhalin ita ta cancanta dani,Mama niɗin ban cika Ɗa ba,na kasa riƙe amanar da aka bani na zabi tsiratar da raina fiye dana Amanata,an yarda dani nayi ha'inci Mama bansan ina take ba,bansan inda zan ganta ba,zuciyata kullum na kukan rashin Amanata ina take?ina taje? Shine abinda yafi tsayamin,a ƙaru na biyu nacin Amana na yarda da wata Amanar Mama bansan ina nayar ba,bansan inda zai nemu wannan takaddun ba,tabbas suna da muhimmanci tunda Daddy da kansa shine ya bani na kula da ita tamkar yadda zan kula da cikina,a kullum nazu cin abinci wannan kalaman sukemin yawu cikin kunena na kasa mantasu"tsagaitawa yay da maganar lkcn da kuka yaci ƙarfinsa Allah yasa babu kuwa cikin parlon duk sun shige bedroom ɗinsu,rumgumesa tayi sosai tana sauraran yadda zuciyansa take ɗagawa,sumar kansa ta shiga shafawa tare da bubbuga bayansa sun ɗauki lkc mai ɗan tsayi kafin taji saukar numfashinsa mai zafi saman wuyanta,sai yanzu ta samu damar zubu da nata hawayen bashi kaɗai yay rashi ba,ita kanta tayi rashin babban yayan nata shi kaɗai take da shine jigunta shine bangun da take jin gina taji daɗi amma yau an wayi gari ta rasashi ta hanyar wasu mugwayen mutanan wanda suka nuna rashin imani a garesa da kuma iyalansa,sosai numfashin da yake fitawr cikin hancinsa ke dukan wuyansa gashi yay mata nauyi haka taci gaba da zama dashi a jikinta.

 JUYAYIWhere stories live. Discover now