Page 5

244 29 2
                                    

AYDANATU 🧕🏽


By ✒️ Malik al-Ashtar

_Love 💓 and very sad 😰 story_ 📖

On Wattpad : https://www.wattpad.com/story/262671816

*PAGE 5*


*HOME OF QUALITIE'S WRITER'S ASSO📚*
_(The Home Of Qualitative Writers That Are Educate Humanities)._
https://www.facebook.com/100495222137315/posts/100496042137233/?substory_index=1&sfnsn=mo

*[📝I.W.A📝]*

Yau Maryam bayan ta aje yara a school, ta shirya zata je Kutiala domin nemo Aydanatu. Tana jin tayi karantawar da zata yiwa labarin domin ta fahimci Aydanatu na bukatar taimako. Tana so kuma zata yi komai ganin ta kai mata dauki, idan ma ta kama zata dauko ta ta dawo da ita wajen ta da zama.

Tana jin kaunar yarinyar har cikin zuciyar tana kuma daukar ta ne tamkar yar uwar ta duk da bata taba ganin ta ba kuma bata santa ba. Wata kila saboda tasha wahala ne sosai, shi yasa Maryam ke son taimakon ta.

Ba zata iya tafiya ba, ba tare da ta sanar da Mahmud ba. Kamfanin da yake aiki ta nufa, ba tare da tasan me zata fada masa ba, bata taba yi masa zancen Aydanatu ba, ko zancen littafin ta da ta tsinta. Tasan Mahmud zai ga wautar ta, wata kila ma ya hana ta zuwa. Duk da haka taje wajen aikin nasa domin sanar dashi tafiyar ta, sai dai da zuwan ta, aka sanar da ita yana meeting kuma babu alamun zai fito yanzu. Ba zata iya jiran sa ba, domin a ganin ta duk wata dakika zata wuce daidai take da rasa Aydanatu. Kiran wayar sa tayi amma a kashe, bayan jira da ta kara yi na rabin awa, ta yanke shawarar yi masa text tare da yi masa bayanin zata je Mali, kuma tafiyar gaggawa ce ta taso ba tare da ta fada masa dalili ba ko yi masa kwakwaran bayani. Tasan zai yi mamakin tafiyar, da jin haushin ta na tafiya da tayi ba tare da sun yi magana ba, kuma da boye masa labarin tun farko.
Komawa tayi gida ta fara hada kayan ta na tafiya, kofa taji ana konkwasawa, taji tsoron ko Mahmud ne. Sai dai tana budewa ta ga Aminatu ce yar uwar ta. Rungume ta tayi da murnar ganin juna.

"Shikenan sai kika manta da ni?" Cewar Aminatu tana mai shigowa daga ciki. "Kin daina zuwa gida na, ga wahalar daukar kirana da kike yi kuma ma idan na kira ki sai in ga kamar hankalin ki yana wani wajen! Meke faruwa ne sis?"

Rufe kofa Maryam tayi bayan ta shigo.
"I'm so sorry yar uwa! Eh da gaske hankali na yana wani wajen, amma kar ki damu ba wani abu bane babba, kuma kin san ba yanda za'a yi na manta da yar kanwata. Kina raina kuma nayi missing din ki nima, koda ban cika nunawa ba."

"Ah please Maryam, kar kema ki fara amfani da kalaman Ibrahim!" Cewar Aminatu tana kokarin hawan stairs. "Haka yake fada domin kara yin nisa da mu, ba tare da muna jin duriyar sa ba, ko sanin dalilin sa ba! Please ke ma kar ki fara hakan, kinsan zaki iya fada min komai, ni aminiyar ki ce kuma yar uwar ki..."

Zata iya boyewa kowa amma banda Amina. Dakin ta ta kaita domin ta bata labarin komai, da shigar su abinda Amina ta fara gani shine akwatin kayan Maryam.

"Shi kuma wannan akwatin? Ko tafiya zaki yi?"

"Ummm ni ban ma san ta ina zan fara miki ba." Maryam ta fada tana sosa kai.

"Toh ai ki fara kawai tun daga farko."

Labarin yanda ta tsinci littafin ta bata, kuma ta bata irin labari mai ban tausayi dake ciki, sannan kudirin da ta daukarwa kanta na nemo Aydanatu.

"What? Kina da tabbacin kin yanke shawara mai kyau na zuwa neman yarinyar nan?" Cewar Amina da mamaki. "Ina nufin... Baki san yarinyar nan ba, ko inda zaki ganin ta a Kutiala! Sis, baki sani ba ko har yanzu tana cen Mali ko kuwa, tunda littafin anan Niamey kike tsince shi, kuma ba wata hujja gare ki ba na cewa wannan ba kagaggen labari ba ne.

AYDANATUWhere stories live. Discover now