Page 11

111 8 0
                                    

🌱🌱🌱🌱🌱

      *SHAREEF*
          _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱

_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*

*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

'''( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)'''

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*



*DATA SHARE*

Call, message or whatsap  07065334256

*MTN*
500MB 150
1gb  280
2gb.  560
3gb.   840
4gb.    1120
5gb      1400
6gb.     1700
Verlid for 30 days.










__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE11*
           Baba ya kasa yin magana sabida jin maganar da Dady ya zo mishi dashi

Sai Dadyn ne yake cewa, "kar ka damu Malam Haruna, ai yanzu mun zama ɗaya, dama ina buƙatar SHAREEF yayi aure a wannan gaɓar, kuma haƙiƙa zan ji dad'i idan har Maryam ta auri ɗaya daga cikin ƴaƴana; sabida hakan zai ƙara ƙarfafa mana zumunci, to na yaba da hankalin Maryam na san zasu dace da ɗana SHAREEF, idan ma kana wasi-wasi ne a kan haɗin, za ka iya faɗan ra'ayin ka ko kuma in turo SHAREEF ɗin ku gana sabida ku san wanda ƴarku zata aura."

"Haba dai? Wlh kar kayi wani tunani a ranka, shirun da ka ga nayi farin ciki ne ya yi min yawa wlh, na san Hafsah zata fi ni farin ciki tunda haɗin zumunci ne babba, Ubangiji Allah ya sanya albarka da alkhairi a cikin wannan auren da zamu ƙulla, gaskiya nayi farin ciki matuƙa." Cewar Baba da rawan murya, yayinda fuskarsa a washe matuƙa da murna

Shima Dady yana murmushin yake cewa, "sai dai alfarman da zan nema shi ne, zuwa gobe zamu tafi Insha Allahu, ko yau ko gobe sai a ɗaura auren su mu wuce da ita."

"To to, ai babu damuwa Alhaji, duk yanda ka ce, Maryamu dai ɗiyarka ce duk yanda kake so haka za a yi, fatana dai a ce mun ƙulla alkhairi wanda zai jawo farin ciki a zukatan mu gaba ɗaya."

Daga haka Dady yace, "a bari zuwa gobe sai a ɗaura auren su wuce, yanzu dai duk a sanar da jama'a tunda ƙurarren lokaci suke dashi".
***

         Koda Baba ya sanar da su Umma Jummai zancen auren, haƙiƙa sun yi farin ciki sun nuna murnan su, barin ma Inna domin tamkar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, yau ga shi ƴarta zata auri ɗan ɗan uwanta, dama a koyaushe tunanin ta da damuwar ta bai wuce inda Maryamun zata yi aure ba, sabida halayyarta na rashin haƙuri, ga rashin kunya da tsiwa, wannan idan bata yi dace da mai ƙaunarta ba a lokaci guda zata cika sa ya sake ta, Maryamu tana da ƙarancin hankali da wauta; girman ne kawai a jiki amma sai rashin jin magana, ta san idan ta je gidan ɗan uwanta zasu riƙe ta amana, musamman ma da ta san Momy Mace ce mai matuƙar kirki da kawaici, tabbas Maryamu ta samu gidan dattako, sai dai kawai halin Mijin ne da bata sani ba har yanzu, tunda ba wai zuwa suke yi ba Yaran shiyasa baza ta iya gane halin kowannen su ba, but tana kyautata zaton samun farin ciki mai ɗaure wa ga Maryamun.


            Dangi sun yi murna, wasu kuma suna ta mamakin yanda auren ya zo a bakatatan, musamman yanda suke ganin Alhaji Ahmed shiyasa suke cewa, "dama kuɗi ai babu abun da ba ya sa wa, Malam Haruna ya siyar da ƴarsa kawai, idan ba haka ba; aure a rana ɗaya kacal? Ai wannan maganar abun duba wa ne."

Babu dai wanda ya saurare su. Don a ranan ma Sadiq da shi da Bashir da Halliru, tunda sa'annin juna ne, tare suka tafi cikin Zaria suka ɗauko Maryamu

Tun a waya Baba ya kira Iya Samira, ya shaida mata halin da ake ciki, farin cikin Iya ba ya misaltuwa, don har guɗa take ta faman yi tsaban murna

SHAREEF 2023Where stories live. Discover now