Chapter 23-24

83 8 0
                                    

༺༻🌹༺༻
࿙꧁꧂꧁꧂࿚
              ֍

*🇰A̺Z̺AℳIN̺*
               *🇳AℳIJI*

࿙꧁꧂꧁꧂࿚
              ֍
༺༻🌹༺༻

*Տᴛ⌾ℛℽ & ᗯℛⅈᴛᴛℰℕ*
            *ɮ̋ʏ̋✍*
෴ℛαвⅈ́'α𝙩 ѕвѕ෴
         ❨ცıɠ ɠᵃ̨ι❩

*©®-Aɴᴀ ᴛᴀʀᴇ Wʀɪᴛᴇʀs Assᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ ✍🏻*
▬▬▬▬▬▬▬▬▬▬▬
➛➛➛➛➛➛➛➛➛➛➛
(wє ѧяє ṭһє ɞєśṭ ѧṃȏṅɢ ѧʟʟ wяıṭєяś)📚
https://mobile.facebook.com/Anatarewritersassocian/
Jσเɳ ɱε σɳ ωαƭƭρα∂:@Bเɠ-ɠαℓ

 
*ʍʀֆ ǟɮɖʊʟʟǟʏ ('ʏǟʀ ʍʊtǟռ ռɨɢɛʀ🇳🇪* ɨռǟ ʍǟtʊզǟʀ ɢօɖɨʏǟ ɖǟ ǟɖɖʊ'օ'ɨռ kɨ ɢǟʀɛռɨ ǟʟʟǟɦ ʏǟ ɖǟʄǟ ʍɨkɨ kɛʍǟ ʏǟֆǟ kɨʄɨ ɦǟkǟ ǟʟʄǟʀʍǟʀ ǟռռǟɮɨ ǟʍɨռ

*ɦǟֆֆǟռ ǟtk* ֆǟռռʊ ɖǟ զօզǟʀɨռ քօֆtɨռɢ.

*🌹ℙaℊℰ❏☞23-24*

        Ba tare da jin komai ba nace masa "yaya na ne" shuru yayi baice da ni komai ba sai ma ci gaba da kallon Ishaq da naga yana yi, yana duban irin kallon da Ishaq yake mun, daga bisani naga ya b'ata fuska kamar yana dad'a nazarin irin kallon da yake mun.
     A hankali nabi kowannen su da kallo take gabana ya fara fad'uwa, tsoro na d'aya kada Ishaq ya k'araso wajen da muke tsaye da niyyar furta wata kalma ta soyayya kaina, naci gaba da zancen zuci tare da addu'ar tsare faruwar hakan.
     Fuskar Nazeem naga ta canja ya duben yace "Anya babu wani abu tsakanin ki da shi kuwa?" take gabana ya fad'i rass! na dad'a tsorata kada ace ya gano wani abu tsakanin mu da sauri na girgiza kai nace "a'a wani abu kuma? Yaya na ne fa" a hankali ya kuma cewa "ina nufin anya bai hana ki tsayuwa da wani ba, ba zai miki fad'a ba kuwa?" nace "ka daina kallonsa baya son yawan kallo in dai ba so kake ya korani cikin gida ba yanzu, kaga bari kawai na koma tun kan ya k'ara so, in yaso mayi waya"
      Sai a lokacin Ummy ta d'ago ta hango Ishaq yana k'ok'arin tawowa wajen mu da sauri ta mik'e tsaye ta k'arasa wajensa.
     Shi kuwa Naazim k'in yarda yayi da tafiya ta ya marairaice "yanzu kina nufin tafiya zaki ki barni tun bamu k'arasa maganar da muke ba, alhalin ban gama jin muryarki ba, kuma ban gama kallon kyakkyawar fuskarki ba? Ki bari ni nayi masa magana na rok'e shi ya kyale mun ke mu gama ganawa"
     Da sauri na fidda kwayar idanuwana waje, fuskata cike da fargabar abinda naji ya fad'a nace "a'a! Kada kayi haka in dai ba so kake ka daina ganina gaba d'aya ba, dan dalilin hakan zaka iya rasani, ba zaka gane bane ni dai nafi so ka tafi zan koma ciki mayi waya" ina gama fad'ar haka na juya na tafi.
       Ina tafe yana bina da  kallo ni kaina ban so na tafi ba shiyasa ma ina tafe Ina juyawa kallonsa, yayin  da idanuwansa suke kaina, shi kuwa  Ishaq ko ta kansa ban bi ba bance masa  k'ala ba nabi ta gefensa na wuce, Ummy tace mun sai munyi waya k'awata itama ta bar wajen ta tafi, har na shige cikin Naazim na kallo na tukunna ya juya ya tafi muka bar Ishaq tsaye shi kad'ai.
     Jikin ishaq yayi sanyi ainun bai tsammanin ganin hakan ba, ba yadda zai yi ala dole ya fuce ya shiga motarsa yaja ya tafi, yana tafe yana tunanin abubuwan da suka faru.
     Ni kuwa bayan dana shiga ciki tsorona d'aya kada na shiga naci karo da Mummy nasan tabbas ba zanji ta dad'i ba, dan haka na salallab'a  na shiga ina sand'a kamar wata mara gaskiya.
      Sai da na fara shiga d'akina na  cire kayana na sake wasu marasa nauyi sabida magariba ta kusa sannan na fito na nufi dining area na fara duban abincin da zanci duk abubuwan da aka shiryawa Ishaq baici komai ba ya tafi bai kuma d'auki komai ba, dan haka na zauna naci duk abinda nake son ci sannan na mik'e na koma sashina na shiga toilet na d'auro alwala.
       Har na gama komai banji motsin Mummy ba, sannan na kira k'anwata Rukhsha tazo na hau bata labarin abinda ya faru, ina cikin bata labari ne kuma naji Mummy ta shigo d'akin take gabana ya fad'i nayi saurin katse hirar da nake, a fusace naji tayi magana "Sannunki har kin dawo? To duk abinda kika yi na sani" wata muguwar fad'uwar gaba naji ya sake yankewa, muka had'a ido da Rukhsha muka kawar a raina nace shikkenan k'arya ta ta k'are innalillahi wa inna ilaihirraji'un, yanzu kenan Mummy duk ta gane shirin da mukai? Wayyo.
      Ina cikin zance da zuciyata naji ta k'ara magana cikin tsawa "wato sabida ba kida mutumci shi ne kika tafi can wajen saurayin k'awarki kika yi zamanki dan kada ki zauna tare da shi ko?" Ina jin haka na saki guntun ajjiyar zuciya a zuciyata nace Alhamdulillah ashe bata gane ba, taci gaba da fad'a "to bari kiji na fad'a miki ko me zaki sai kin aure shi indai Ishaq ne dole ki aure shi sha-sha-sha wadda bata san kanta ba, in banda ma wauta da shurme waye zai k'i d'an uwanshi yaso wani bare? Mazan da akasarin su na yanzu ba suda tabbas, shurmen banza kawai to bari babanki ya dawo gwara suzo ayi magana da wuri in yaso naga ta tsiya".
       Take na fudda idanuwa na bak'in ciki ne yabi ya cika min zuciya ban san lokacin da nace "haba Mummy nifa ina da wanda nake so yanzu fa ba'a yiwa mace auren dole Mummy dan Allah ki kyale ni na auri wanda nake so" Tunda na fara magana tayi shuru tana kallona dan bata tab'a tsammanin zan fad'a mata haka ba ta k'ara hasala yayin da na kawo nan a zancena tace "kin gama maganar? nace kin gama? fitsareriya, har yaushe kika zo duniyar da zance ga abinda ya dace kice ke ga abinda yafi miki dacewa?"
    Sake magana nayi "Mummy ki fahimce ni nifa bada wata manufa na fad'a ba dan Allah ki kyale Ishaq nifa zan zauna da mijin ba wani zai zauna mun da shi ba" sosai ran Mummy ya b'aci tace "toh uwata gwara da kika fad'an tunda ke kika haifi kanki ko ke kika haifen" Ruksha ta kasa cewa komai sai hak'uri da take ta bawa Mummy ni kuma tana d'an tab'ani da k'afarta alamar nayi shuru karna k'ara magana, duk da haka bakina ya kasa rufuwa nan na fara k'unk'uni ina magana a ciki-ciki , "ni gaskiya Mummy bana son shi wallahi bana son shi kawai nabi umarnin ki ne, amma ni ina da wanda nake so?"
     Ran Mummy ya k'ara b'aci ta k'araso inda nake fuskarta cike da mamaki ta kai mun wani wawan mari har sai da na daina gani daga bisani kuma na dawo na fara gani, zuciyarta ta k'ara hasala cikin zafin rai ta runk'a magana "idan kin isa ke 'yar halak ce to ki sake wata maganar, marakunya futinanniya ina magana kina magana ke har wuyanki ya isa yanka, Allah ya shirya mtsswww..."
    Ta fuce ta bar d'akin ranta yana k'una, ni kuma na kwanta nan ina sharar kuka Ruksha na bani hak'uri tare da ce mun "duk laifinki ne yaya da kinyi shuru da hakan bata faru ba" Ina shash-shek'ar kuka Ina magana "yanzu sai na zauna a auran Wanda bana so kenan? Wallahi ba zayyu ba ko me zai samen gwara ya sameni akan me? Wa zai zauna mun da mijin ?" Naci gaba da kuka, ita dai Ruksha tama rasa me zata ce tayi shuru daga bisani kuma ta mik'e ta futa.

           ✹❀✹❀✹❀✹

   Ishaq na tafe yana tunani bai san lokacin daya ture wani mai machine ba sai da mutane suka fara taruwa ya ankara yayi saurin dawowa hayyacinsa da sauri ya futo daga mota yana salati, su kuwa sauran jama'a an samu abin nema sai k'ara taruwa suke masu k'ok'arin d'auka a waya sai d'auko wayoyin su suke.
     Waje ya runcab'e ana neman ba'asi wasu kuma na k'ok'arin d'ago me machine daga k'asa wasu na k'ok'arin d'aga machine d'in, kan kace me waje ya runcab'e wasu na cewa karya hak'ura wasu kuma na bada hak'uri.
     Shi da kansa Ishaq d'in hak'uri yake bawa mai machine d'in, yadda Allah ya taimake shi ma shi mai machine d'in baiji wani ciwo ba, kuma shi kansa machine d'in babu abinda ya same shi dan haka mai machine yace babu komai ya hak'ura haka Allah ya tsara.
     Nan dai suka fahimci juna har ishaq ya bashi wasu kud'ad'e mai machine yace ba zai karb'a ba, wasu suka runk'a ya karb'a amma yak'i karb'a, wannan  yasa Ishaq ya zaro card d'in sa ya bawa mai machine kodan watan wata rana, ganin haka yasa kowa ya watse daga wajen ya kama hanyarsa ishaq da mai machine ma suka yi musabaha kowannen su ya tafi.
     Ishaq bai isa gida ba sai bayan Kiran sallar magriba, yana shiga kai tsaye ya wuce sashen mahaifiyarsa, ya tarar da ita tana sallah gefe guda na makeken falon gidan.
     Zama yayi kan d'aya daga cikin kujerun dake kewaye a falon har sai da ta sallame.
      Tana idarwa ya durk'usa k'asa ya gaida ita wannan al'adarsu ce na kowacce sallah sai an gaisa da juna, tayi masa maraba da dawowa, sai dai kuma taga fuskarsa ba kamar yadda ya futa cikin farin ciki da walwala ba.
       Fuskarta cike da rashin fahimta ta  tambaye shi abinda ya faru da shi, nan ya fara yi mata bayani cewa "ni Ina ganin Mummy ya kamata a kyale batun wannan yarinyar" Haj.Zulaihat tace "ban gane a kyale maganar ba" Shuru Ishaq yayi na d'an wasu dak'ik'u kafin yace "Mummy bana son abinda zai lallata zumuncin dake tsakaninki da 'yar uwarki, yarinyar nan bata sona da bakinta ta fa'dan bata sona kuma a gabana naga wanda take so d'in , ni Ina ganin kawai a kyale maganar dan Allah na samu wata wadda nake so".
     Haj.Zulaihat tayi shuru na mintuna sannan ta kad'a kai fuskarta cike da tausayin d'an nata tace "shikkenan kayi biyayya baka yi musu da zab'in da nayi maka ba, sai ma nuna soyayyarka ga abinda na zab'a maka wannan tunani ne mai kyau, ba komai insha Allahu zaka samu wadda ta fita ni daman sha'awar da nayi maka kenan dan kar a samo mara tarbiyya tunda yanzu zamanin duk ya sauya akasarin 'yan matan yanzu ba suda mutunci ba suda tarbiyya duk d'abi'un su sun canaja da ayi zab'en tumun dare gwara a d'au na gida da aka yarda da tarbiyyarsa, ba wad'anda zaka auro k'arshe kayi daka sanin auro su ba"
     Ishaq yace "insha Allahu zan samu ta gari kici gaba da yi mun addu'a Mummy ki kuma daina damuwa, Ina son Naazneen amma zan danne zuciyata insha Allahu na kawar da sonta amma dan Allah Mummy ina neman wata alfarma guda d'aya" Haj.Zulaiha tace "wacce alfarma kenan?" Ishaq ya dubeta yace "karki fad'awa iyayenta abinda ta fad'an dan bana son ace ta dalilina wani abu ya faru da ita" Haj.Zulaihat tace "karka damu ba zan sanar da su komai ba, kaje ka nemi abinci kaci ka manta da komai kar kasa hakan a ranka" ishaq ya mik'e tare da fad'in "insha Allahu Mummy zanyi yadda kika ce" mik'ewar Ishaq keda wuya yaji wayarsa tayi k'ara➦➦➦➦



    *YAWAN COMMENT YAWAN TYPING✍🏻*





🌹☞ℬıɠ ɠᗅ̨ι *¢ɛ✍🏻* *_2020_*

K'AZAMIN NAMIJIWhere stories live. Discover now