CUTAR DA KAI EPISODE 8

933 15 1
                                    

💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

Free Page 8

*PAID BOOK*

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim

"Wannan  littafin na kudi ne  ,mai bukata karanta shi  zai  tura 500 ta wannan   account number  din  1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an  tura sai a turawa  wannan  number alert  +234 803 238 4602   domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi  sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne .  "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi  za'a iya tuntu'bar  Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos  lace da kamfala  ,Lagos rapa , jaka da takalma , getzner na cotonou da  chiganvy, volyal lace  duk akan farashi mai sauki ,ga mai  bukatar  siyan ɗaya ko sari  yayi magana ta wannan number 08059623096,yauwa har ma da agwalumar  cotonou mai dan Karan zaki muna turawa kowani gari ...🥰🥰

"Kuka  take  sosai  tana  tunanin  rayuwarta  data gabata  , isa  izza  da  jiji da  kai  ko  yar  sarauta  iyakarta   kenan  , dayawa  mutane  ada can  baya  sun sha  faɗa mata cewar da  gidan  sarauta  aka  haife ta  ba'a  san  abinda zatayi ba,ita kanta tasan gidan sarauta ne   yafi  dacewa daita  saboda karfin  mulkin dake tattare  daita, taja numfashi a hankali  ta  sauke tana ciza gefen labenta na kasa sai ga wasu sababbin hawaye masu zafi  sun gangaro mata  ."

"har  ga  Allah  bata  marmarin   sake  yi masa  rashin   mutunci  saboda ta  horo iya horowa akanshi ,  tana  tsoron sake  faruwar  wani abu saɓanin  zaman lafiya , shiyasa  da zasu zo kasar   aunty  ummi  bata  so  ta  biyosa ba  , taso  ya  barta a kasarta  ne  ta cigaba da rayuwarta  a gaban iyayenta  domin  tasan  zasu  taimaka mata ,dan bazasu  yarda wani  mummunar  abu ya sameta  ba, duk lalacewar  itace din rayuwarsu ce amman ta nace lallai sai ta biyosa wanda ita a tunaninta kasancewarsu guri daya  zai sa ta  janyo hankalinsa gareta a she bata sani ba  cikin ukuba ta jefe  kanta     ta  karasa  maganar cikin wani  sabon kuka ."

wani  kullin tashin hankali   ta dinga  ji a cikin  zuciyarta  ,a ranta tace  "Aliyu  baya qaunata  sai wasu hawayen sharrrrrrr tamkar an bude famfo , tana  jin motsin saukowarsa  amman taki fitowa daga bayi  dan tasan  idan ta fito ma  wani  sabon  bakinciki zai kusan  mata , kuma  tasan wannan fitowar da yayi    gidan nawal    zashi  dan   ya kuntata mata , sai  data tabbatar da ya  bar gidan gabadaya  sannan ta mike ta isa bakin fomfo ,ta kusan minti biyar a jikin famfo tana wanke fuskarta , addur kariya da zaman lafiya a tsakaninsu tayi yafi sau babu adadi sannan ta  fito parlour  ,ta cigaba da sheshekar  kuka, ranta na wani  irin quna  ta zauna  hawaye na sake bin kuncinta ,da zarar ta runtse idanunta babu abinda take gani sai  kyakkyawar  miskilalliyar fuskarsa mai nuni da babu wani abu da ke damunsa . "

tana  cikin  wannan halin taji  motsin  buɗe  kofar falo  da  sauri ta bude idanunta ta  soma ƙoƙarin  goge   hawayenta  da  hanzari safiyya  ta karaso cikin filin falon  tana  tambayarta  "lafiya me kike  ma  kuka  kisna "?wani  matsanancin kuka ne  ya  sake  kufce mata haka  yasa hankalin safiyya  sake tashi "wai meke  faruwa  ne  kisna ki  faɗa  min me ya faru  kike kuka "?

cikin dasashiyar muryarta  da bata fitowa  sosai  tace "ba abinda ya sameni  juyin duniya safiyya  tayi da kisna domin  jin abinda ke faruwa  amman  taki faɗa  mata  dan haka Safiyya  ta bige  da rarrashi  har ta samu tayi shiru  "kin ma ci abinci kuwa  ta d'aga mata kai  ba dan  ta sakawa cikin komai  ba , ruwa safiyya ta tsiyaya mata a glass cup  ta mika mata  ,ta amsa ta  sha  kadan sai lokacin taji zuciyarta  ta ɗan yi mata sanyi  ,cikin natsuwa safiyya tace "ki ƙara hakuri kisna duk da kina boye  min abinda ke damunki  amman zuciyata  na faɗa min kina cikin damuwa mai tsanani wanda kusan ina ganin hakan  a zahiri ,dan duk sanda zan zo gidan nan sai na iskeki cikin tashin hankali da damuwa ".
"abinda nake son dake  Ki ƙara  hakuri kowace mace da kika gani  yanzu hakuri  take a gidanta ,ba wai  wani dadi take ji  ba, kowani  ma'aurata da irin  tasu matsalar , idan kikaji matsalar  wata  zakice naki  ba komai bane, sannan idan  kina
lura zaki ga  kowace mace  a gidan aurenta tana  da katuwar matsala ,  idan  aka tara miki  matan duniya babu mace  guda  daya da za'a  cire  wacce bata da matsala  a rayuwar aurenta, haka idan aka tara mazan duniya kowane  dana shi matsalar , abinda  ya kamata  muyi  shine hakuri  ,ki karfafa zuciyarki  ki  daina wannan  kuka  babu abinda Aliyu yake so a rayuwarsa  kamar ya ganki cikin damuwa da tashin  hankali  , mai yasa  bazaki d'aurewa zuciyarki  ki  fita lamarinsa ba , duk abinda kika san hakinsa ne ki sauke masa kiyi  lamuran  gabanki , wallahi  muddin yaga kin fita hanyarsa kin sharesa  zai dawo hankalinsa dan yaga kina yawon  damuwa   idan ya bata miki   ."

CUTAR KAI Where stories live. Discover now