36

7.7K 746 299
                                    

UWA UWACE...36

Batul Mamman💖


Addu'ar samun rahama da kyakkyawan makwanci ga iyayen 'yan uwa da muke tare. Sisters Teema (mahaifi), Hadiza Yauri (mahaifi) da Hashal (mahaifi da 'yan uwa maza uku). Allah Ya jikansu da rahama Yasa sun huta.


***
Da sallamar da ya san babu mai amsawa ya murda hannun kofar dakin. Fitila a kunne take da alama cikin sauri aka manta ta. Ga kaya watse a ko'ina. Riguna ne da wanduna harda kwalaban turare na jiki da na kaya. Salihi ya yi ajiyar zuciya ransa duk babu dadi. Da kunnuwansa yaji Mubashir yana waya da abokinsa suna shirya yadda zasu fita party shadayan dare. Bai yi masa magana ba domin yana son tabbatarwa kansa Mubashir din zai je ko kuwa. Fitar da ya yi niyya ya fasa ya zauna a gidan ba tare da sanin dan nasa ba.  Goma da rabi kuwa sai gashi ya fita daga gidan da sand'a a zatonsa babu kowa sai Ummule da ta dade da kwanciya.

Wata leda mai kyau Salihi ya gani a saman tebur din da Mubashir yake ajiye tarkacen makarantarsa. Ya dauka ya bude yaga sababbin takalma kala biyu da risit din sayayya. Abin da aka kashe na sayayyar ya girgiza shi. Bill ne na dubu casa'in da yan canji a sayayyar kaya. Shi dai bashi da kudin da zai iya bashi ya yi sayayya mai tsada haka. To a ina ya sami kudin?

A dakin yayi zaman jiransa har bacci ya kwashe. Goshin asuba ana tsaka da kiran sallah sai gashi ya shigo da sand'a. Rufe kofar yayi da sauri ya murda mukulli sannan ya kwantar da bayansa a jikinta yana ajiyar zuciyar tsira.

"Allah Ya soni Baba bai tashi ba"

"Ko kuma ni Ya soni da na kwana a dakinka ba."

Wani wawan juyi Mubashir ya yi a matukar razane yana kokarin murda mukullin kofar ya fita amma ya kasa. Ilahirin jikinsa babu inda baya ji yana rawa.

"Juyo ka dubeni Mubashir."

Maimakon ya juyo sai ya cigaba da kokarin fita har Salihin ya tadda shi inda ya juya masa baya. Hannunsa dake rike da mukullin ya kama ya rabasu da yatsun nasa. Sau daya ya murda su duka suka ji sautin budewar kofar. Mubashir dake faman gumi zuwa yanzu ya sake kama hannun kofa wannan karon. Shi fa burinsa ya bar gaban uban ko ta wane hali. Saboda shi da kansa ya san cewa bai taba yin laifi kwatankwacin wannan ba, shi yasa hankalinsa gabadaya ya tashi. Gani yake suna hada ido zai gano duk abubuwan da suka wakana a wurin party din.

"Irin wannan patin kuke kira till dawn ko?"

Shiru babu amsa daga Mubashir kuma har yanzu hannunsa yana jikin hannun kofar amma ya daina murdawa.

"Ban hanaka zuwa ba jiya bayan na gama jin shirinka da wani a waya."

Ras, ras, ras...haka gaban Mubashir ya cigaba da faduwa yana sauraron mahaifinsa a tsorace.

Salihi ya daure zuciyarsa iyakar dauriya saboda warin hayaki iri iri da yake ji a jikin Mubashir. Da wahala idan bai sha kayan maye ba ko tarkacen hayakin. Sassauta murya ya yi sai ka rantse kuka ne zai kwace masa a kowane lokaci.

"Tsakaninka da Allah Mubashir idan ka kwatanta abin da akayi a wurin da kaje da tarbiyar addini da ma maslahar zamantakewar dan Adam kana tunanin Annabin Rahama zai yi maraba da kai?"

Fada, mari, zagi, tsinuwa ko duka sune abubuwan da yasa rai dasu. Ko kadan bai yi zaton wadancan kalaman ba. Daga kai ya sami kansa da yi ya kalli babansa. Duk wani zafin kai na matasa sa'anninsa sai ya kufce masa. Rashin kunyar da aka koya masa koda zata baci irin yanzu yaji babu guda da zai iya. Allah SWT Yafi komai da kowa. Sunansa kadai da aka ambata gami da kwallar  disappointment a idanun mahaifinsa sun dagula masa lissafi. Ba yadda ya iya dole ya girgiza kai a matsayin amsa ga tambayar da aka yi masa. Ta yaya ma zai yaudari kansa yace inda yaje bai sabawa musulunci ba?

UWA UWACE...Where stories live. Discover now