Թɑցҽ 8

1K 55 1
                                    

      *INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*

      {Onward together}
*{ we give the reader's of ours the best out of the best's,, our inks are melodious And dropping a kinda light's to reader's}*
'''THE PEN OF LOVE 😘 HEART TOUCHING ❤ TEARS OF SORROWS😭 CURDLES 😊 GIGGLES 😁 AND MARRIAGE THINGS 💑'''
*JUST GIVE US FOLLOW.....*✔

                      💥

        ❄️❄️❄️❄️❄️❄️❄️❄️
            *Ḧ̤Ï̤B̤̈B̤̈Ä̤T̤̈Ṳ̈L̤̈L̤̈Ä̤Ḧ̤*
              ❄️❄️❄️❄️❄️❄️❄️

          *°•(ĸyaυтa daga Aℓℓαн)•°*

   *°ιиιqυιту,ємραтну,нυмιℓιαтισи & яσмαи¢тι¢ ℓσνє💑°*

*MALLAKAR:HAFSAT HAFNAN💕*

        *WATTPAD:HAFNANCY:*

*°ѕα∂αυкαяωα gα Dr. υмαя fαяυq вαнαgσ,ємιя σf иιgєя ѕтαтє,мιииα*°
____________________________________

                            💥

      *Թɑցҽ 8⃣*

   Najmiy kuwa tana shiga b'angaren Haj.Babba taji wani uban kuka ya taho mata,sam bata lura da Haj.Babba da kuma Haj.karama dake zaune afalo ba,sai kuma ƙuyangun dake durkushe agabansu suna musu hidima,masu firfita sunayi,haka kuma masu tausa nayi.ko lura dasu batayi ba dake makeken falo ne,ta nufi dakin baccinsu da gudu tana 'yar shessheƙa.

   Haj.karama ce ta soma hango bayanta tana wucewa zuwa daki da dan gudu-gudu.Cike da tashin hankali ta dubi Haj.Babba wacce bata masan abinda ke faruwa ba sai aikin baiwa wata ƙuyangi order take dake mata tausa.Tace"Yaya kalli auta can ta shigo da gudu kuma kamar ma kuka take... "
    Agigice Haj.Babba ta dubeta tace"Ina autar take?"

"ta shige daki.. "acewar Haj.Karama

   "maza Maymunerh tashi muje mu dubota nidai Allah yasa lfy dai... " Haj.Babba ta fadi hakan tare da mik'ewa at once,suka sallami kuyangu,kana suka nufi hanyar dakin da Najmiy ta shige da sauri saurinsu.

    ***
Bawan Allah kuwa Hayat yana nan zaune dai inda Faruq ya barshi,zuwa yanzu hawayen ya daina zubo masa,sai saukar da numfashin da yake tayi da karfi,acikin wannan halin ne su Jabir suka shigo suka riskesa,acikinsu babu wanda ma ya lura da yanayin da yake ciki don suna shigowa ko hada idanuwa dashi basuyi ba suka zube ak'asa,kafin Jabir yakai ga magana tuni yaji Hayat yayi saurin katse masa hanxari"Jabir wai sau nawa ne zan gaya muku cewar ku dena zub'e min ak'asa?karfa ku manta dani daku duk daya muke awajen Allah,wanda kawai yafi wani matsayi awajensa shine wanda yafi tsoronsa,kuma ko ba komai ai ni din k'anin bayanka ne na nesa ba kusa bama,don Allah ku daina bana so,pls get up immediately.... "

    Allah sarki!ta inda kuma suke son Hayat kenan,sam bashi da ganin kansa azuwan shi din wani ne,infact yama daukesu kamar yan'uwansa ne.

Jabir yace"Allah ya taimaki jarumin jarumai,amatsayinka na dan sarki ya zama dole kaima mu girmamaka,don haka kayi haquri bazamu iya dainawa ba...... "

   Bai tankashi ba,ya dauki ruwan faron dake gabansa,ya balle marfinta,sai daya furta"Meke tafe daku yakai amintaccen Abba mai martaba?" kafin yakai bottle din bakinsa.

   Jabir yace"Allah yaja da ran Yarima Karami,ga sako zuwa gareka daga mai martaba,yace yana nemarka da gaggawa..... "
   
     Da sauri ya cire bottle din daga bakinsa,ruwan kuwa ya kwareshi sosai wanda ya janyo masa wani mugun tari har idanuwansa sukai jajawur,duk kuma adalilin tashin hankalin daya shiga ne,hakan na nufin Faruq yakai kararsa ne koko menene?don fitarsa kenan baa wani jima ba sai ga dogarai wai mai martaba na nemarsa da gaggawa kuma yanxun nan.

HIBBATULLAH Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang