69

2K 169 0
                                    

🔺6⃣9⃣🔺
Bayan sun gama murnar da suke yi ne suka ci abinci sukayi zaune suna hutawa,yayinda sukaji sallama,sun amsa sallamar ne tare da kai duban su gun qofa sai suka ga wani hadadden gaye mai kyau dashi da ganin sa ba zai wuce 27yrs ba.

Ya shigo dauke da murmushi a fuskar sa ya russuna ya gaida su Alhj Basheer.
   Tare da fadin  i'm pharmacist kabeer Abubukar Abdullahi ,nazo ne dmn na bawa patients magani.
   Alhj Basheer yace bismillah
Pharmacist kabeer ya qarasa gurin Nusaiba tare da ajiye ledar magunan da ke hannun shi kan drawer,ya zuba ruwa a cup tare da miqawa Nusaiba hade da 6allah magani ya bata,ta kar6a tasha ya shiga 6allo mata sauran maguna yana bata,bayan ta gama ne ta miqa masa cup, sai kawai cup din ya subuce mishi sai kan jikinta,tace"ah meye haka ta fadi hakan ne tare da share ruwan da suka zuba a jikinta, yace"sorry kafin yake fitar da handkerchief ya miqa mata ba tare da yace mata komai ba sai kyawawan idanun sa da yake kallon ta dasu, Nusaiba ta kalle shi kamar kar ta kar6a sai kuma ta sami kanta da kar6ar handkerchief din,
ta goge jikinta ta miqa masa tare da fadin tanks.
    Sannan ya koma gun Imtihal dmn ya bata nata maganin.
    Imtihal ta kalle shi ta kuma kalli Afnan.

Afnan yace bani maganin na bata, dmn wannan hukuma ce shan maganin ta sai da rarrashi.
   Pharmacist kabeer ya bashi maganin.

   Afnan ya kar6a tare da zuba ruwa a cup ya 6alla magani ya ba Imtihal.
  Imtihal ta wani  turo baki tana kallon maganin  ba tare da ta kar6a ba.
    Afnan yace my imtee kar6i kisha.
   Marairai ce masa tayi tace please yaya Afnan ni ba sai na sha magani ba, sbd en qana nan raunuka ne fa kawai dani.
  To ai ko qananan raunuka akan sha musu magani.
    Um um nidai kayi haquri kar na sha.

     Alhj Basheer ne yace kar6a mana kisha kinji.
   Ba musu ta kar6i maganin tana ji kamar tayi kuka wanda da runtse2 ido da komai ta samu da qyar ta hadiye maganin.
   Nan pharmacist kabeer yayi sallama da Alhj Basheer.
   Alhj Basheer yace dashi"ko doctor Hakeem yana office? Eh yanzun na bar sa a office dmn shi ne ma ya turo ni nazo na basu magani,eh ya sanar dani cewa zai turo a basu magani.
   Amma nafi buqatar ya sallame mu gabadaya shiyasa nake son na same sa.

Nan suka fita tare.

Alhj Basheer ya tafi office din doctor Hakeem,tare da nuna masa buqatar sa akan yana son a sallami su imtee.

   Doctor Hakeem yace gaskiya Alhj bai kamata a sallami dayar yarinyar nan ba, sae dai dayar wato wacce ke dauke da qananan raunuka.
    Alhj yace ok ai indai har zata sami kyakkyawar kulawa a nan ba matsala bane,doctor Hakeem yace sosai inshaAllah zata sami kulawa, bare pharmacist kabeer din nan da yaje basu maganin mutum ne mai kulawa sosai  shiyasa nake so ya riqa bata magani dmn ko kadan baya wasa da aikin sa.
  
  Nan alhj Basheer yace ok to yayi sannan ya masa godiya ya fice.

A 6angaren su Hajiya hasina kuwa an jima sosai kafin ake fitowa da kamal daga gurin theater.

Sai dai bai farfado ba hakan yasa tayi zugum cike da damuwa tana kallon shi.
   Abban kamal kuwa wato tsohon mijinta bai ma san da cewa an fito da kamal ba,sbd koda aka fito dashi yana gurin sallah.
   
A 6angaren su Nusaiba kuwa kullum pharmacist kabeer ke zuwa yana bata magani,
Wanda har sai da ta cika sati daya sannan aka sallame ta.
       Imtee kuwa tun a wannan ranar tabar asibiti aka tafi da ita gidan Abbanta Alhj Basheer ,wanda har gagarumar walima Alhj Basheer yasa aka shirya,
en uwa da abokai ba wanda bai zo ba,ciki har da Islam wacce tayi farin ciki sosai.

Yau satin ta daya a gidan, yayinda take samun kulawa sosai a gurin su har dai a gun en biyu da basa barin ta tayi komai,komai su keyi mata,har abinci suke dafa mata,amma kafin ta samu taci sai sunyi ta rigima Zeenat tace nata za'a fara ci,Zarah tace sam bata yarda da hakan ba nata dai za'a fara ci,imtee kam abun har dariya yake bata da mamaki.

Ko yanzu  kuwa abinci ne suka kawo mata sai rigima suke da juna, Hajiya zainab ce ta shiga yi musu fada,tace"wai ku yaushe ne zaku san kun girma kullum abu daya kuke tayi, har ma kuna hana ta samun natsuwar cin abinci,maza Ku fita!
    Imtee tace ai mama da kin bar su,hajiya zainab tace ai yaran ne ba'a biye wa ta kansu,dmn duk tsawon nan da kike gani har sun kai Nusaiba, tsawon dai ne, amma ba shekaru girma ya riga wayo shiyasa kullum suke ta miki aikin yara.
    Mama yi haquri dai su zauna,,.Aa ai naji ma Nusaiba sai faman kiran su take tayi tun dazun,kuje can ita zata iya fama daku....kubar imtihal ta huta ko don tsohon cikin da ke jikin ta, zeenata tace  don Allah mama ki bar mu a nan baza mu dame ta ba wlh, kuma yaya Nusaiba da ta koro mu shine take wani  neman mu,,, ita Nusaiba? Eh mama wai fa muna kallon wani  hadadden film shine kawai muka ga pharmacist kabeer yazo, mu kuma mukayi zaman mu dmn mun dauka cewa lokacin shan maganin ta ne yayi,shine fa ta dalla mana harara wai mu tashi mu bata guri,,,umma tayi murmushi tace Allah dai ya shirya min ku, amma pharmacist kabeer ne zai xo gidan nan a dalilin me,, wlh umma da gaske muke gaya miki, girgiza kanta kawai tayi ta fice tare da basar da zancen su.

Imtee ta jawo hannun su ta zaunar dasu suka shiga cin abinci.

Yau kusan sati biyu kenan imtee na a gidan su sai hutu take ba alamar zata koma gidan Afnan,Afnan kuwa sai damunta yake kan yana son yazo ya dauke ta amma taqi.
              
          *********

Umma ce zaune a falo tana karatun wani  littafin addu'o'i Afnan ya shigo fuskar sa a daure da shigar sa ko zama bai yi ba yace, wai umma yaushe ne imtee zata dawo, nifa gaskiya ina buqatar ta dawo,sbd ina buqatar ta a kusa dani,ni kadai a gida ba dadi, ko wai dai sun manta cewa da aure a kanta...Umma ta kalle shi da mamaki tace tunda sun manta ai sai kaje ka sanar dasu,tunda rashin kunya ke damunka da rashin haquri, umma na fayi haquri...sati biyun ne kayi haquri, kai ko tunani baka yi!kasan basu ta6a rayuwa da yarinyar nan ba, don tayi sati biyu gurin su kake ganin har an takura ka.......wayar ta ce tayi qara koda ta duba Hajiya zainab ce maman Imtihal,da fara'ar ta ta daga wayar wanda sun
jima sosai kafin suke gama wayar.
    Umma Ta kalli Afnan tace"to kama ji,
hajiya zainab tace da dare kaje ka dauki matar ka Imtihal,sai dai suna buqatar idan imtihal ta haifu ka barta taje gurin su dmn yin wankan jego.

     Sosai yaji dadi,amma zancen wankan jegon nan bai masa ba, yace
"amma umma meyasa idan ta haifu baza tayi zamanta a gidana ba?sbd tafi samun kuluwa a can,kuma gashi gidan naka ita kadai ce se kai,to umma ai zan iya bata kulawa kuma ga indo sai ta je gidan namu,kinga ai ko haka din yayi dmn ko Islam da ta haifu a gidan suraj tayi zamanta sbd tana da er aiki.... ai Islam da Imtihal ba daya bane kuma ai ita indo auren ta ya matso kusa,wai har auren ya matso kusa amma ummà kamar na ta6a jin auren indo da jinawa sosai? kwarai kuwa ka ta6a ji dmn har auren an daura, a ranar da aka daura auren ango ya kwanta ciwo, ciwon da bai tashi ba kenan Allah ya kar6i ransa, to tun a wannan lokaci zafin mutuwar sa bai bar indo ta kula kowa ba,sae yanxu ko shi da qyar yaci nasara ta amince.
    Da kuma matasawar iya talatu dmn da ta kanta ne da tuni indo tayi aure har ma da yara.
   Afnan yace to Allah ya taimaka ni zan fita.

Da dare Afnan yaje ya dauko Imtihal suka tafi nasu gidan.

Kowa ya tafi nasa daki dmn watsa ruwa.

Imtee ta fito daga wanka ta gama shafa mai, ta jawo rigar baccin ta tare da zare towel din jikin ta,kafin ta saka rigar, Afnan ya shigo dakin,
kallo daya tayi masa tare da juya bayanta sannan ta saka riga.

Afnan yayi zaune kan bed yana jiran ta gama  shirin kwanciya su tafi dakin shi,sae kawai yaga tayi kwanciyar ta ba tare da tace dashi komai ba.

Yace"my imtee daki na zamuyi bacci fa"ni yau a nan nake so nayi bacci, meyasa my imtee? Haka naji ina ra'ayi, kuma ka fita ni ina son zan rufe daki dmn bacci nake ji sosai,murmushi yayi tare da kwanciya kan gadon yace nima a nan zan kwana, ya fadi haka ne tare da qoqarin jawo ta jikin sa,wani  kallo ta masa cike da tsiwa kallon ya ba Afnan mamaki sosai dmn bata ta6a masa irin sa ba, tace"ka fitar min daga daki, da mamaki yace imtee me yake damunki yau? Ko wani  laifi na miki ne da ban sani ba,dan guntun tsaki tayi ta tashi ta dauki pillow zata fita Afnan yayi saurin riqo hannun ta, yace"yi haquri kinji gaya min mene ne,jin tayi gabadaya ya takura ta ta lumshe idon ta cike da damuwa tare da furzadda iskan bakinta a hankali,tace please yaya Afnan ka fita!zai yi magana kenan tayi saurin dora yatsanta kan lips din sa tace please ka fita kawai, Afnan ya fita dakin cike da mamaki,yayinda imtee ta rufe qofar dakin taje tayi kwanciyar ta.

IMTIHAL (COMPLETED) .Where stories live. Discover now