*COLONEL UBAIDULLAH*
( _the story about a young gentle man_)*ᏚᎢᎾᎡY ᏔᎡᏆᎢᎢᎬN ᏴY*✍🏻
*Z͢A͢H͢R͢A͢ A͢B͢D͢U͢L͢* (ᴹᴼᴹᵞᴺ ᴬᴴᴸᴬᴺ)
( *y̾a̾r̾ s̾a̾r̾a̾r̾i̾n̾ k̾a̾i̾n̾u̾w̾a̾*)
👸🏻 *SAHIBAR KAINUWA*👸🏻_dedicated to my brother_
*U̶B̶A̶I̶D̶U̶L̶L̶A̶H̶I̶*
~~•~~•~~•~•~•~_my wattpab_@Fateemah0
~~•~~•~~~•~~•~~•~~~•
*_Tun daga wannan page din har izuwa karshen wannan book din na ku ne my 5 stars._*✨*My Doter Samira bint Abdallah*✨💋
*Dear Fatima Bintu Sagir*✨💋
*Sisina Farhat Mrs M'J*✨💋
*Antyn Ahlan Princess (Nafeesat)*✨💋
*Habibty احلام فاطمة*✨💋
💞💞 Naji dadin karar'ku a gareni son so domin Rabbi, Allahu ya taya muku.💞💋🙌🏻*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________**🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*_Na so na kira sunayenku wa inda suka min sharhi a page din da ya gabata kafin wannan amma Allah bai yi ba, dan haka duk wacce ta min sharhi ta saka a ranta wannan page din kyauta ce gareta, kuyi yadda ku ke so da page din dan naku my ppl's ina so ku sani ni Zahra Abdul Momyn Ahlan taku ce inayinku._*💋
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*page°°°°°76&80*Kira Abi'atu ke yi ba ƙaƙƙautawa, sai da ta yi masa kira wajan takwas amma bai daga ba, dan lokacin da ta yi masa kiran farko da ya gani yayi tsaki sai ya mai da wayar cikin aljihun wandonsa, ya juya yana ba wa sojojinsa umarni.
Kukan tashin hankali Abi'atu ta saka gami da cewa.
"Yaya Safwa bai ɗaga ba fa, wayarka kuma netwrk ya dauke ya ƙi kawowa kwata-kwata!"A fusace Safwan yana jan mota yana kan bin wa inda suka kwamushe Hafiza ya hau saukewa Abi'atu ruwan bala'i yana mata masifa dan hankalinsa a tashe yake ,domin ko da ya iskesu ance sarkin yawa ya fi sarkin karfi, su bakwai, shi ɗaya ai ba zai iya ba, idan aka taki rashin sa'a suka kashesa suka jinkiɗar da Hafiza da Abi'atun ai an bata goma ɗaya bata gyaru ba, sannan ace zai fara biyawa kiran yan sanda ai kafin su iskesu sun yiwa Hafiza Illa idan ma an kamasun kenan, dan yasan by tym da zasu iso idan aka ta ƙarƙare sun gudu.
"Iskancin banza da hauka! Numbern Mijinki amma ba ki da shi?Mijinki fa!? Da ace kuna da number juna har za ki din ga yi masa wannan kiran bai ɗaga bane, da ace kuna da numbern juna ya ga wannan kiran da kike masa yasan babu lafiya, ai sai ki ci gaba da kira, ko kuma ki nemi nerwrk a wayana ki ci gaba da kira, in kuwa ba haka ba, muna karasawa sai su kashemu duka a huta, mtswwww!"
Kira Abi'atu ta ci gaba da yi tana kan kuka.Ubaidullah jirgi ya shige ya zauna, ana jiran jama'a su gama shiga jirgi ya tashi da zarar lokacin tashinsa ya yi, dabara ce ta faɗowa Abi'atu da sauri ta tura masa saƙo da cewa.
" _*KAYI WA ALLAH DA ANNABI S,A,W) KA DAUKI WAYAR NAN, IDAN HAR BA KA ƊAGA BA, ZA A RASA RAYUKA (ABI'ATU CE)*_" ta tura masa, Ubaidullah ya ciro wayarsa yana shirin kasheta gaba ɗaya ya ga tarin miss calls da numbern dazu, mamakinsa bai gushe ba sai ga shigowar saƙo buɗe sakon ya yi, ya karanta sannan ya shiga wajan history yana shirin kiranta sai ga kiran nata na sake shigowa, ɗagawa ya yi, muryar kukan ne ya fara kaiwa dodon kunnensa naushi, gabansa ne ya shiga bugawa a kiɗime ya ce.
"Abi'ah! Meya faru? Meya sameki? Wa ya taba miki?" cikin sheshsheƙar kuka ta ce.
" *DAN ALLAH! DAN ALLAH! IDAN HAR JIRGIN'KU BAI ƊAGA BA KA DAWO AKWAI BABBAR MATSALA AN DAUKE HAFIZA!*" wani wawan zabura Ubaidullah ya yi ya miƙe da gudu yana buge mutane, yana sauƙowa daga step din jirgin Sojojinsa ne suka kallesa "Mota" shi ne kawai abun da ya iya furtawa, nan aka miƙa masa Mota ya shige ya bata wuta, cikin tashin hankali Ubaidullah ya ce.
" *SU NA INAAAAA! INA ZASU KAI MIN ƘANWATA!?*"
"gamu nan mu na kan bin su ni da Yaya Safwan, kayi amfani da location, Dan Allah kayi sauri kar su cutar da ita, ga mu nan dai sun dauki hanyar fita daga cikin gari" da sauri Ubaidullah ya yi connecting yana bin su da gudu, sai ka ce zai ta shi sama jikinsa sai bari yake yi, hankalinsa idan ya kai dubu to a tashe yake.

YOU ARE READING
COLONEL UBAIDULLAH
ChickLitlabari ne akan wani saurayin Soja akwai (tausayi soyayya cakwakiya hassada munafurci kar dai na ciku) kudai ku bibiye labarin