GN-08

1.9K 233 25
                                    

Ina kallonta sai tausayinta da nawa ya rufe ni, ban san lokacin da na fashe da kuka ba na dafe kaina.

“Kai Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”

Na fada cikin kuka, sai Adnan ya nufo ni yana fadin.

“Yi hakuri Momy sannu”

A zatonsa ciwon da nake masa ina na na dazun da ma fada masa ban sda lafiya ne yake damuna. A dole na share hawayena na kirkiro murmushi na mike tsaye na nufi inda Namra take.

“Kin tashi?”

“Ya jikin?”

“Bana jin ciwon komai”

Ta fada tana ta kallona da idonta da sukai ja saboda bachi, sai kuma ta kwanto da jikinta jikina.

“Bari na kawo miki wani abun ki ci kinji yar kirki”

Ta gyada min kai sai dai ina sauka mikewa tsaye daga kan kujerar sai ita ma ta sauko ta matsa kusa da ni kamar zata shige cikina.

“Zauna bari na kawo miki”

“A'a Uncle Abdallah yace ya daina bari kina yin nisa da ni duk inda kika je na biki ko da gurin aiki ne idan ba haka ba Baba Sadi zai iya zuwa ya yanke ni saboda na fada”

Kamin nai wata magana Adnan ya nufo inda mike da sauri yan zaro ido.

“Baba Sadi ne zai yanke ki? Mi kika fada”

“Ba komai, zo muje”

Hannunta naja ban bari ta sake cewa komai ba. Na nufi kitchen din da ita.

“A cikin gidan nan wani be isa ya zo ya taba ki ba, ke ba a nan ba ko a wani wajen ne wani be isa ya taba ki ba, ki kwantar da hankalinki kinji yar kirki”

Na fada mata ina kokarin zuba mata abincin, sai ta fara motsa ido.

“Mama ina jin tsoro”

“Ai Baba Sadi be san kin fadi wannan maganar ba, kuma ba fada masa zan yi ba dan haka ki kwantar da hankalinki kinji?”

Ta gyada min kai, a plate na zuba mata abincin sannan na janyo hannunta muka fito falo, zaunar ita nai ina kokarin bata abincin sai ta ce.

“Momy ban wanke baki ba”

“To je ki wanke”

Bata min musu ba ta tashi zuwa cikin dakinsu, daman can Namra ba yarinya ce mai kiriniya da jan magana ba, ko abu yake cinta yana da wahala ta iya fada ga ladabi da hankali kamar ita ce yayar Adnan, duk abunda na saka ta sai ta yi ba musu idan nace daina zata daina, ga jinkai duk abunda ta samu ita dai Momy dai Momy dai. Rashin ji da kiriniya sai Adnan shi da yake babba da Aiman dakr binta sai kuma wannan yar berar nan Amal ita kam fitinar ta tafi ta kowa ga barna komai ta dauka sai ta lalata.
  Wayata ce dake kan dinning tai kara, sai na aje plate din a kasa na tashi na nufi inda wayar take, number Abdallah ce har na yi kamar ba zan dauka ba idan sai kuma wata zuciya tace min na dauka wata kila wata maganar ce aka Namra.

“Assalamu Alaikum”

Na masa sallama da sanyayyiyar muryar da ke fassara irin damuwar dake tare da ni, domin bana da wani sauran kuzari a yanzu. Sai da yai shiru for few seconds sannan na amsa min.

“Wa'alaikissalam Halima ya jikin Namra na san ta farka yanzu ko?”

Na gyada kain kamar yana gabana, shi kuma kamar ya san abunda nai sai ya ce.

“Good ki yi hakuri na fada miki magana marar dadi dazun, rai na ne ya bace shiyasa, kuma dan Allah Halima karki saka damuwa a ranki, karki kamar ba zaki iya ba, kina da yan'uwan da zasu iya goya miki baya ki yi komai, karki bar Baba Sadi ya ci bulus”

GOBE NA (My Future)Where stories live. Discover now