page 46

92 6 0
                                    

🅰 *S🅰N🅰DIN GROUP*🙊🙊

*Written by*
 
💅💅 *SADNAF*💞

  *PURE MOMENT OF  LIFE WRITERS*

    _We don't just entertain and educate we touch the heart of the readers_  *P.M.L*

*A short story based on true life story*

*Page:-* 46

Yanzu ke hajia Kaltume kinsan iyakar zunuban da kika dauka kuwa a dunia,kin zama hangar shedan,kina bin yaran mata da manyan mata kina lalata masu rayuwa,kina koya masu zina,kina bata kananun yara maza ta hanyar koya masu mummmunar dabia ta zinace zinace, kina bata rayuwar aure (babbar sunna ta maaikinmu) kina wulakanta daraja da martabar aure,kina koya ma matan a al-umma ha'intar aure alhalin babu abinda mazajensu suma gaza dasu,ke koda sun gaza ki sani zina haramun ce kuma babu inda aka halatta komin tsananin condition kuwa
Hajia Kaltume ki sani ga abinda Allah ke fada akan irinku nan
_Innallazina yuhibbunah an tashi'aal fahishata fil lazina amanu lahuum azabunn aleemun fid dunia wal akhira,wallahu ya'alamu wa antuum laa ta'alamuun_
*(Hakika wadanda suke son yada alfahasha ta (zinace zinace) a cikin mutanen da sukayi imani, lallai suna da zunubi mai tarin yawa a dunia da lahira. Allah masani ne akan abinda baku sani ba)*


Dan  Haka Ku tuba Ku nemi yafiyar Allah tun mutuwa bai riskeku a cikin irin wanan halin da  kuka jefa kanku a ciki ba,yanzu mijinki kina ganin kinyi masa adalci,yanzu idan na tona miki asiri na yad'aki a gidan duniya na nemo mijinki na fad'a masa abinda kike aikata wa zakiji dadi,?" Da sauri Hajja Kaltume ta girgiza kai tana kuka dan tunda Yusuf yafara magana taji wani tsoron Allah na shi garta bata tab'a nadamar abinda take aikatawa ba sai yau

.Yusuf magana ya cigaba da yi yana

Ina ma ana yiwa mazinata hukuncin tun a gidan duniya kafin su mutu,da an rage zinace zinace a duniya,Allah ubangiji ya shiryeku idan kuna da rabon shiriya, Ku sani duniya ba gidan zama bane,Ku farka tun da wuri,dan kun shagala da yawa, naseeha Yusuf ya ringa musu sosai,Hajja Kaltume dasu ton g suka ringa kuka,suna nadamar abinda suka aikata,Yusuf sim card d'in wayarsu ton g ya cicire ya mik'a musu yace musu tafiya zai yi da wayarsu bazai iya basu ba,zai basu kud'i su siyi wani wayar, kallon Hajja Kaltume yayi data d'urkushe tana ta kuka yace " kiyi k'ok'ari ki nemi yafiyar mijinki dan kin cutar dashi,kin ci amanarsa ko da kin tuba kin nemi yafiyar Allah kindaina abinda kike yi,matsawar baki nemi yafiyar mijinki ba Allah bazai yafemiki ba har sai kin nemi yafiyar mijinki,a k'arshe ina baki shawara ki rufe wanan grp d'in da kika bud'e idan ba haka ba,duk wacce ta cigaba da iskanci asanadiyarki kina da zunubi babba,kallonsu Ton g yayi yace " Ku kuma kun maida zina ado,kun maida zina abun burgewa,kuje ku sab'i Allah kuzo kuma kuna fad'a kuna turawa junanku hotona da videon abinda kuka aikata,karku manta kowane gabb'a na jikinmu zai  yi shaida ranar Lahira ina jiye muku zaman wuya,ina jiye muku daren hisabi daren da bawa ya kan yi kuka,daren da mata zata ga mijinta ta ringa b'uya akan Hisabi,daren da d'a zai ga ubansa ya ringa b'uya akan hisabi, daren da 'ya taga uwarta ta ringa b'uya akan Hisabi,Allah ya ganar daku gaskiya,ina mai Baku shawara kuje Ku nemi duk mazajen da kuka aikata zina da matansu Ku nemi yafiyar su,daga haka ya fice daga d'akin yace Wani acikinsu ya biyo shi ya basu kud'in wayar,gabad'aya Yusuf ya d'auresu da jijjiyoyin jikinsu an rasa mai tashi a cikinsu ya bishi, kuka suke sosai suna tsinewa Hajja Kaltume dan duk itace silar jefasu a cikin wanan masifar,yanzu dagaske suma sai an nemi matansu,yanzu dagaske suma in suka haifi 'yaya sai an neme su,( Sadnaf kuwa tace wanan dole ne ai duk    abinda kayiwa d'an wani sai anyi maka)..........................



*HAUSA NOVELS* 📚
*HAUSA NOVELS* 📚📚
*HAUSA NOVELS* 📚📚📚

A SANADIN GROUPWhere stories live. Discover now