page 3

6 0 0
                                    

©️®️Amjad...

      💋JANAN💋
(The Captain Family).

Ban yiwa kowa alqawarin samun yanda yake so ba a book dinan ,Sede nayi muku tanadin Zazzafah Kuma tsaftacacciyar Soyayyah me tsayawa azuciya ,Kudai ku biyo alqalamina .

This book isn’t for free it’s just 500 Contacts me via 08100312134 charts only no calls.

Page 03.

Ya sallam ya furta ahankali yana lumshe idanun shi ,Shi ya kasa gane inda Ummah ta dosa ganin yakeyi da ita da Anty da Momy  ai duk daya ne to duk wannan abun na Mene ,cin abinci a wuri ta shikenan seya zama matsala ?

Dagowa yai ahankali yace “Ummah nifa banga abun daga hankali anan ba dake da Anty duk daya na daukeku case closed “

Ya fada yana mikewa ya fara kokarin fita adakin . Yanada zuciya muddin yace ze zauna zaayi batacciya yanada zuciya da In har ta baci shi Da kanshi baya iya controlling dinta ,shiyasa yake gudun duk wani abu daze Masa kutse cikin farin cikin sa .

Binshi ummah tayi da ido bakin ciki yana turnuk’eta ,duk akan wannan mayyar matar ne gashi yaronta datafi kauna yana nuna Mata tafishi muhimmanci.

Kallonta Ihsan tayi tace “Ummah kema da baki mishi magana ba kinsan halin Yayy”.

Kallonta Ummah tayi tace “Toh Ihsan ya kikeso nayi wannan Matar me take nufi damu ne agidannan ta kwace me gidan mun barmata shima d’an nawa bazata barni dashi ba ,so take kowa seta rabani dashi “.?

Ummah ta karasa har muryanta na rawa tsabar yanda abun ya Mata tsaye a zuciyarta ,

“Ummah kiyi hakuri tunda kinsan dai ba haka ta barsu ba kema da kanki kin sani ,kuma ai ramin karya kurarre ne “.

“Ihsan ita nata ramin bana tunanin k’urarre ne wanann cin zalin tunda tazo gidan nan take yinshi gashi ta doshi shekaru ashirin yaushe kike ganin zata bari “.?

Shiru ihsan tayi tana karajin tausayin Ummah yana ratsata tabbas ko su suna ganin yanda Dady yake rawar kafa akan Anty ,

Koda ya fita part dinsa ya wuce zuciyar shi na mishi nauyi , shiba mutum bane meson hayaniya ,yana matukar kokari wurin ganin yabawa kowa muhimmancin sa agidan amman ya lura Ummah batason ya rab’i Anty ko kadan ,wanda besan menene dalilin ta ba . Shi koma mene bayaso su ringa sakashi aciki shi namiji ne wanann abun nasu baze shiga ciki ba so yake kawunan su ya hadu .

Harya karasa part dinshi tunani ne fal acikin zuciya da ruhin shi ,so yake ummah ta fahimce yanda Anty takeda matukar kirki kuma take kaunarshi .

  Abude ya tarar da kofar part din ,ya murda handle ya shiga angyara part din tsaf komai an maidashi muhallinshi,se jerin luggage dinsa da suke a parlour da alama Abba me bawa flowers ruwa ne ya shigo dasu kamar yanda ya umarcesa.

Bedroom dinsa ya nufa Seda ya kwabe kayan sa ya shige toilet yadan jima kafin ya fito ,be wani dauki lokaci me tsaho ba ya shirya cikin kananun kaya da sukayi matukar karbar shi ,suka fito da zallahn kyaun da ubangiji ya mishi .
   Ko part din Ummah be koma ba ya karbi makulln Motor a hannun driver ya shiga yabar gidan .

Rai abace Ummah ta fito daga part dinta ‘ko sallama batayi ba tafada dakin tana huci tun daga kofar parlour ta fara cewa “kina ina munafuka mayya “.?

Da sauri Anty ta mike tana binta da kallo alokaci daya tana had’iye wani kululun abu a makoshinta jin sunan Da ta kirata dashi ,duk da ba bakon ta bane ta saba dajinshi,amman setaji yau zagin ya taba zuciyarta

  Har tsakiyar parlour Ummah ta karaso tana nuna Anty da yatsa.
  “Wallahi wahainiyar ki ta kiyayi ramata,tun ban miki abunda zakiyi kuka ba da idanun ki ,ki dauke idanunki akan d’ana ahiirr dinki Wallahi idan zaki cinye kurwar kowa to ki kiyayi ta d’ana Mayyah dangin sadaka yallah “.
Ummah ta fada tana barin dakin kamar kububuwa yanayin tafiyarta kawai ze tababtar maka da yanda ranta yake abace.

JANANKde žijí příběhy. Začni objevovat