LAILAH-DIZHWAR

1.9K 82 2
                                    

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
            🌷🌷🌷🌷🌷🌷
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
            🌷🌷🌷🌷🌷🌷
   *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*
    *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*
         *_ZAINAB NASEER SARKI_*
             *_ (ZEENASEER😘)_*
          🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*

*(21)*

__________


Kobayan an gama Walimar da Memartaba ya shirya, kowa gida ya nufa, yayin da Dizhwar yana zuwa, abinci aka kawo masa, sai bayan yaci ya koshi yasha magani ya kwanata.

_________
Mama kuwa tun bayan da Lailah ta tafi gashi time din anyi magriba, tashi tayi ta fita waje dan ganin bata dawo bah,
  Kasancewar tasan gidan su Rauda ta tafi shiyasa bata wani damu sosai bah,

Abu kamar wasa har goma tayi shiru, kasa zaune tayi bare tsaye, Daidai lokacin Babansu ya dawo.

Nan ta nuna masa ai Lailah bata nan har yanzu bata dawo bah,  dan haka shima fada ya kama yima Maman akanme zata bari ta fita duk da sunsan Lailah yarinyace me hankali bazasu zargeta bah.

Shiru suka zauna ganin bata dawo ba har 11pm, hakan yasa Abban ya fita.

Kai tsaye gidan su Rauda ya nufa, koda yaje gidan kulle da kwado babu kowa, wani gumine ya karyo masa.

Yana kokarin tafiya saiga Rauda ta dawo.

Ganin shine yasa ta gaida shi, nan ya hau nuna mata Lailah bata zo bah.

Haka itama ta maida masa, dan raban da taga Lailah ta jima dan ita yanzu daga wajan aiki take ba wajan biki bah.

Batare da yace mata komai ba, ya tafi hankalinsa a mutukar tashe, gashi Lailah bata taba musu irin haka bah.

Haka ya dawo gida duk jikinsa a sanyaye, tunda Mama taga ba Lailah ta fara kuka, nan ya zauna tare da sanar mata be gan ta bah, kuma ba gidan su Rauda taje bah.

Kuka Mama ta fara tana nuna hannu alamun dama saida jikinta ya bata karya tayi mata.

Nan de suka rasa abunyi, suka hakura zuwa wayewar gari, amma koda garin ya waye, duk da ba wani baccin kirki sukayi bah,
  Safiya nayi Mama ta tashi Abban dole sai sunje wajan yan sanda sun sanar musu da batan yar tasu.

Haka ya hakaru suka je,
  Suna zuwa kuwa suka samu wasu anan waje suka fara nuna masa magana da kurmanci, kasancewar be gane abunda suke nufi sosai bah, suka dauko musu biro da Paper dan su rubuta abunda ya kawo. Su.

Nan suka zauna Abban ya rubuta yakai musu.

Bayan sun gama karantawa, suka maido musu da amsar ko tana da saurayi.

Nan suka rubuta tana dashi amma dan gidan sarkin Zamfara ne.

Koda suka karanta abunda Abban ya kuma Rubutawa, kallan Juna sukayi, tare da fadin,

_"Amma wannan mutanan basu da hankali, taya zasu ce mana dan sarki ne yake san yarsu, kode dan sarkin mahaukata"_
  Haka suka kora su daga police din suka fita suna Rokonsu amma babu wanda ya kula su.

Mama zama tayi tana ta faman kuka, ganin abun yaki karewa yasa Abban,fada mata suje su Sami Aminu.

Kallan sa kawai tayi, tare da goge hawayanta ta tashi tayi tafiyarta ta barsa anan dan koda Lailah mutuwa tayi bazata nemi daya daga cikin yaran nasu ba, balle kuma bata tayi tana sa ran insha Allah zata dawo gareta.

________
Har yamma tayi anata faman shagali a gidan Sarki domin yaune za'a kai Amare gidan su.

Gaba daya an gama shirya wa su Jafar Jirgin tafiyarsu.

LAILAH-DIZHWAR Where stories live. Discover now