MATAR MIJINA

927 54 0
                                    

❣❣ LABARIN AURENA❣❣

Nah
      Khadijah Ahmad

    

                  91-95

    "Ban hanaki shan ruwan lipton ba, Meyasa kike son b'atamin rai ne?" ya k'arasa maganar cike da damuwa, sunkuyar da kai nai, hawaye ya cika min ido,  numfashi ya fursar ya zagayo ta bayana na zama a tsakiyarshi ya zuro da fuskarshi ta wuyana
  "Kinsan bansan kuka ko," yatsun sa ya saka cikin sumar kaina bakinsa daidai kunnena cikin maraitacciyar murya yake magana
  "Hearty u r d cause of ol dis nine ya kamata na shiga wani hali ba ke ba, ke murna ce ta kamace ki, ya kamo sangalalen hannuna, kingafa yacce kika koma meyesa hearty uhm, shafo fatar k'irjina yayi look hatta ga nan se da ya fad'a"  kuka nane ya 'karu

"Shhhh.." Ganin bazan daina ba ya had'e bakinmu gu d'aya ya shiga kissing d'ina tenderly wanda yasani manta wani damuwa"..

   Please hearty kada ki ke zama da yunwa ko da daddare ne kika ji yunwa ki nema ba kice saida safe ba na ajiye miki ruwa da flask na ruwan zafi kayan tea na kan centre table duk a gefen gadon uhm?" Gyad'a kai nayi ya bani peck a fuska "saida safe"

  "Allah ya kaimu" ya fice, har  zan sa key ya bud'e" and again dan Allah karki saka wannan zulumbuwar  rigar gobe" dariya nayi had'e da girgiza kai, zai juya nace "wait,"tare da manna masa sumba a fatar baki, har cikin zuciyarsa yaji dad'i kar kibar key a jikin k'ofar kar nazo kina bacci, "ok" ya fice, na koma  kan kujera na zauna bayan na kunna akwatin talabijin dan kallon tauraran d'an adam, wuraren goma da rabi na kashe komai na nufi d'aki kwanciya raina fal farinciki bama idan na tuna irin soyayyar da muka zuba yau da yamma wacce muka jima bamuyi irin ta ba.

~
  Ta 'bangaren zamana da Aneesa ba matsala saidai tun lokacin da ta cika wata guda ta fara canja min, har yakai batason taga Najib tare dani ko yayi zancen wani ikon Allah kuma shi Najib a lokacin sai ya koma komai ni, ya manne min har cemasa nake kai wai kamar bame mace biyu ba, yakan yi dariya yace ni MIJIN MACE 'DAYA(rufaida omar)ne kuma kece, ke Aneesa fa sai ta canja min duka a da lokacin da aka kawo ta nakan danne kishina na je wurin ta muyi yar hira wacce ita da kanta tayimin magana kan cewa bana zuwan mata, amma yanzu idan naje ma da sagaggiyar gwiwa nake dawo wa dan kallon arzi'ki bana samu, da abun ya isheni nayiwa Najib magana ta'be baki yayi yace
"kunfi kusa"

   A kwana a tashi ciki ya bayyana jikin Aneesa zo kiga murna wuri na  mama kuwa har sadaka tayi saidai abun mamaki shi uban gayyar ko ajikinsa wai an tsikari kakkausa, dana sameshi nayi masa magana kan abinda yake baya dacewa gwasaleni yayi ban damu ba saboda inda sabo na saba indai kan Aneesa ne haka yake min, cikin Anesa mai kwad'ayine tsirfa kala kala, dan haka kullum cikin aike nake in kuwa abun ya juyo mata har su pizza takeso kuma tace home made haka zan wuni a kitchen sai ya zamana na daina samun time d'in kaina har ma da na mijina wanda ke wata uwa duniya aiki, ko da yazo gari ma mama bata barin mu tare sai tace muje sashen Aneesa koda zata buk'aci wani abu,. Akwai wata rana da hearty zai dawo daga lagos kamar yacce na saba na shiga had'a masa delicious abincika dana san yafiso na tsala uwar kwalliya na hakince a falo banfi minti biyar da zama ba saiga kiran mama wai nayi maza nazo sashen Aneesa a rikice na fita ina shiga tace
  "Yawwa zauna ki matsa mata k'afa wai ciwo take mata" da sauri na d'ago kai ina kallon mama,
  "A a yakika tsaya yi maza mana", zamana keda wuya mukaji 'karar motar Najib, wucewar mintuna ashirin sai gashi..wani irin kallo yake bina dashi me wuyar fassarawa saidai kana kallon kwayar idonsa kasan tashin hankaline kwance cikinsu,

  "Ga auta ga auta, sannu da zuwa ya hanya", numfashi yake tun karfi kan ya ansa ya dawo da idonsa kaina ke tashi anan" ya fada a tsawace!

  "Bangane ta tashi ba bakaga abinda take bane?"

  "Nagani mama shiyasa nace ta tashi,"

   "To isashshe nice nan na sata,"

   "Ki tashi nace!!" A firgice na tashi, maganar Aneesa ce ta dawo damu
  "Wash Allah mama 'kafata", mama tashiga tafa hannu

You'll also like

          

"Laahaila haillallahu, Auta yaushe ka zama haka kaine kake musayar yawu dani?" Ta fashe da kuka , a rikice na koma ina matsa 'kafar

   "Mama dan Allah kibar kuka kinga fa inayi wullahi bazan bar nan ba saida yardarki"

  "Mamaa..shikenan ai ta zauna kibar kukan hakaa dan girman Allah kiyi hakuri" cikin sheshshe'kar kuka tana goge hawaye da bakin zani tace

"Uhm rayuwa oh ni d'iyar nan..."

"Mama kiyi hakuri nace wullahi bazan kuma ba" ya fad'a a raunane, "ya wuce, ta kalleni idan ya lafa mata ki d'an gyara mata gidan sai ki kwana wurinta saboda yanayin jikin!" Dass! K'irjina ya buga kan na amsa
"To mama," da mamakina sai jin dariyar Aneesa nayi 'kasa 'kasa, kallonta nayi nan ta faki idonsu tayimin gwalo, wani bak'inciki naji ya taso min kamar na rufeta da duka na lumshe idona ina tausar zuciyata had'e da ambaton sunayen ubangiji, a ranar ko kallona Najib kasawa yayi dan ya danganta lefin a kanshi sai zuwa shabiyu suka tafi na rufe gidan  ina juyowa da niyyar shiga d'akin dana rakata ta kwanta sai mukai kicib'is ga mamakina sai jinayi ta rungumeni
  "Yeey...today will be fun gani gaki under dsame roof wullahi ina murna ko ya kika ce aminiya" ta wani kyaftan ido cike da takaici na rafka mata harara had'e da jan tsaki na samu kujera na zauna, kwashe wa tayi da dariya tana tafa hannuwa mrs Najib, ta zauna kan centre table tana facing d'ina had'e da crossing legs sai faman 'kas 'kas take da chewingum nidai se binta nake da kallon tsana can ta nisa,

  "Tsk tsk tsk, Sorry 'kawas yaune kad'ai zan tsai dake shima dan inason passing miki information ne, ta rangwad'ar da kai gefe, Naila u did a huge mistake by trusting me!, harararta nayi ta cigaba!

    "Wani lokaci daya wuce na kasance hatsabibiyar yarinya mara jin magana harka da maza na d'auketa  tamkar ruwan sha, nayi fitinar dani kaina banajin Allah zai yafemin(waiyazubillah) kawai dai ayi sha'ani kingane ai, nakan raka maza garuruwa dama garin tafiye tafiyena Allah ya had'ani da wani babban soja ya nemi na rakashi lagos, da isarmu nayi gamo da katar wanda kallo d'aya nayi masa naji duk duniya ba wanda nakeson kasancewa dashi sai shi bawai dan inasonshi ba sai dan kurum sha'awarsa hahaha...ba kowa bane wannan gayen face ur beloved hubby Najib!!, yacce akayi nasanshi kuwa ni da kaina naje har office dinsa na nuna masa kwad'ayina a fili yak'i na nuna masa zan shiryu inhar yayarda zaiyi tarayya dani nan ma yak'i hakan yasa na rink'a bincike a kansa dake Allah na k'aunata sai ya had'ani dake nayi miki dabarunmu irin na 'yan bariki har kika zama silar sada ni da muradina, gashi yanzu nasamu abinda nakeso har na gode Allah n d funny thing is dat huh bafa karatun gaske nake bafa dan tunda naganshi tare da ke na wurgar da komai nahau fighting for abinda rai ke sha'awa, woah and to tell u d truth mummy na ba mahaifiyata bace hasalima shes my mate i mean tare muke buga runs d'inmu na nuna miki ita a matsayin  mahaifiyata ne saboda ki kara yarda dani haka lokacin da akazo neman aurena hayo mutane mukayi, waima ke Naila banda shirmenki taya za'ayi ayi maganar aure da shagali cikin sati biyu kacal!, ni alokacin da kikayi min magana idan baki manta ba ai inata k'i da naga kin dage yasa na yarda tunda nima inaso na samu abinda na jima ina nema"' ,..ta tsugunna a gabana, dan Allah Naila ki min hanyar da zan fita a gidannan wullahi nagaji ina buk'atar d'and'ana wasu mazan gashi ban saba zama gu d'aya ba pls help me pls"

   Zuciya ta ce kad'ai bata buga ba amma na tabbata a lokacin jinin jikina ya k'afe dan tsabar firgicewa da kalaman ta na shiga rud'u numfashi na ya rink'a fita dakyar hawaye kuwa kamar an bud'e ruwan famfo. Maganar da ta fara had'amu da ita na tuna, farkon had'uwarmu, in kuwa ban manta ba a tsukun nan Najib ya dawo.
  
    ~"he's back" yanayin kallon dana  bita dashi yasata saurin d'aga hann sama "hey hey..ba wabi abu bane prince charming d'ina ya dawo, after a long period zamu sake had'uwa, bara na wuce sai mun had'u gobe~

Jin ana jijjigani yasa na dawo da idona kanta cikin d'aga murya tace "bakiji abinda nace bane" k'arfi nasa na hankad'eta na nufi k'ofa

  "Kika sake kika fita wullahi sai na fad'awa mama"

Sulalewa nayi a gun ina wani irin gunjin kuka had'e da tausayawa mijina da ni kaina da kuma mama

  "Tsk tsk tsk poor Naila, ina me shawartar ki da kada kiyi gangancin fad'awa mama maganar nan dan kallon wacce ke d'awainiya da kishi zatayi miki, afterall nike mulka zuciyar mama saboda d'an jikallenta" ta k'arasa maganar had'e da shafo cikinta, nan ta shige d'aki ta barni, ranar haka na kwana kuka kamar raina ze fita idan na tuna da cikin jikinta kuwa sai inji haushin kaina had'e dana mijina badan komai ba sai dan yacce har ya iya tarayya da karuwa!!!.

   Washegari ina sallar asuba na k'alk'ale ko ina kamar yacce mama ta umarceni da nayi shida daidai na nufi sashena a falo na tarar dashi ya rafka uban tagumi da sauri ya nufo ni hannu na d'aga masa na shige d'aki a guje nasa key biyoni yayi yana bubbuga k'ofa

  "Hearty bud'e k'ofar dan Allah kiyi hak'uri bani da yacce zanyi ne mama ce tace dole"... Bud'e k'ofar nayi da k'arfi na rufe k'irjinsa da duka, kyaleni yayi be hanani ba har na sulale ya tsugunna kusa dani "indai hakan zai huci zuciyarki dan Allah ki k'arasa" d'ago rinannun idanuna nayi cikin sheshshek'ar kuka nace
   Dan meyasa kasan wacece Aneesa ka yarda ka had'a jiki da ita kuma kuma...gashi  ta samu ciki..whyyyyy...."

Wani malalacin murmushi yayi, "Alhamdulillahi, since she hv managed to tell u her self, d'ago fuskata yayi, fuskarsa cike da annashuwa yace
   "Naila zaki iya yarda idan nace ban tab'a sanin wata mace ba bayan ke?" Ido na zuba masa ban ko motsa ba,

"Well sincerely speaking ban tab'a kwanciyar aure da Aneesa ba,dalilin dayasa na amince da auren ma saboda kwanciyar hankalinki ne amma bari kiga.." tsam ya mik'e na bishi da ido zuwa can ya dawo d'auke da farar takadda ya mik'o min a sanyaye na bud'e...

©Kdeey😊

LABARIN AURENAWhere stories live. Discover now