CHAPTER FIFTEEN

1.3K 89 0
                                    

*💦WACECE ITA? 💦*

*PAGE 37*

*NA UMMU ZAYD*👌🏼

*Kuyi hakuri kuyi maneji da wannan wlh abubuwane sun sha min kai fatan zaa gafarceni*

Amarya ta tare a dakinta ranar farko abinda yafa ra ba zee mamaki be wuce yanda mardiyya take commanding muq ba tunda isarsu wanda hakan ba karamin mamaki yabataba sosae, a gajiye take don haka bata tsaya wani tunani ba tashige bangarenta da muq din ya nuna mata, sallolin da ake binta kawae tayi tabi lafiar gado, sosae tayi barci don sae wajen laasar ta tashi ta yi sallarta sannan ta shige kitchen dinta saboda tasami abinda zata dafa tanayi tana mamakin muq din itada take amarya amma sam tunda ta shigo be leko ta ba jikinta a sanyaye ta daura jollof din sphagetti dayaji beef tareda dauko lemun exotic ta jera a tray tayi parlourn ta tana ci tana kallo wanda hankalinta sam ba a kallon yake ba, bayan ta kammala ta jai kayan kitchen ta wanke sannan ta dawo dakinta tasake shiga wanka tareda cancada ado cikin wata atamfa super holland sosae tayi kyau, har akayi ishai zee na zaune tana jiran ango amma shiru hakan ba karamin kona mata rai yayi ba matuka don hka tsam ta tashi tasaka hijab tareda zuwa main parlourn su, abinda tagani ba karamin mamaki yabata ba muq yana duke yana ta faman goge ma mardiyya kayanta itakuma hakimar tana kwance kan three seater din parlourn tana kada kafa,fon purnishment din da takeson bashi kenan na fanshe haushin kishiyar dayayi mata don sunada me masu wanki da guga, kallon kayan tayi jibge guda a kalla zae iya kai karfe dayan dare be gama ma zufa kawae yake sharcewa iya gajia ya gaji amma be isa yace ya gajin ba ga yunwa na nukurkusar shi don rabon dayaci abinci tun na jirgi. Matsowa zee tayi tareda fadin:man menene haka kake yi amma kasan yau ni bakuwa ce gidannan sae ka tafi ka barni nikadae sannan kuma kazo kana guga daga dawowarka ko hutu babu, kallon gefen da mardiy tae yayi wacce take kokarin tashi daga kwanciar datayi don ta lura dole ta taka ma zee din birki"ke dakata ! sauraramin kada kizo kina kawomin tsohon karuwanci gidana bakisan da muq din da ke kanki duk karkashin ikona kuke ba na daga maki kafa ganin ke bakuwa ce amma na lura sam baki da kunya ?! Zeena da tsananin mamaki yakama tayi tsaye batareda ta ce komae ba yasa takalli muq "tashi mutafi nace maka ! Kamar wawa haka yayi tsugune yanajiran order daga yar mulki,bacin rai yasanya zee juyawa a fusace tayi hanyan dakin ta, mardiyya ta barke da daria, aranta kuma tana mamakin Meyasa aikinta beci kan zee din ba sabda yanda karkuzu yafada mata tsoronta zata dinga ji amma saetaga akasin haka tattare da zee din, don haka ta tashi tsam tashiga bedroom tareda latso number din karkuzun, hallo ranka yadade amarya fa tazo amma sam bata tsorona gani nake kaamr aikin nawa beyi ba, karkuzu yayi wata budurwar daria "mardidi manyan mata bayau aka kawota ba kijira gobe kiga abinda zae faru kit yakashe wayar hakan ne yasa ta bi wayar da kallo tareda dan kishingida hankalinta ya dan kwanta  barci tuni yayi awon gaba da ita dama salla bata cikin kayanta ita kanta tamanta yaushe rabonta da sallar ko saduwa sukay da muq din ba wankan tsarki takeyi ba saedae muce Allah kyauta.
A vangaren zee kuwa bayan tashige daki wani irin kuka ne ya kufce mata saboda tsabar bacin rae sosae take kuka wannan wane irin kaddara ce ta sameta mijinta yazama baiwar mace sae avinda aka ce yakeyi first rananta a gidan miji amma sam babu abin tunawa najin dadi sae damuwa tuni danasanin auren muq yafara tsartuwa aranta, maganganun ummi suka fado mata a rae "zee bawae muq din bane banaso harga Allah inason yaron amma inamaki tsoron zama da kishia"a lokacin saedae tayi daria gani take kishiya ba wani abin tashin hankalinta bace tunda muqaddas din yanasonta ita ma tanasona sannan tana da kudi, sae gashi tun kan a je ko ina tunaninta yazama karya, cikeda rashin kwarin jiki ta tashi ta shiga toilet ta dauro Alwala ta fara jera nafila akan Allah yamata saukin wannan jarabawa tata, anan kan dardumar barci yayi awon gaba da ita, muq bae gama gugar ba sae wajen sha biyu da rabi na dare sosae jikinsa ke ciwo ga wata irin azabar yunwa yanaji hakanan ya tashi ya zare socket din dayayi gugar tareda fara kwashe kayan gugar yakai dakin uwargida, yajera mata su tsab a cikin wardrobe ganin dayayi tana barci ne yasanya shi jan jiki a hanakli kamar munafuki ya nufi dakin zee, murda kofar yayi yaji ta bude don haka sadaf sadaf yashige dakin, dirrect kitchen dinta ya nufa yaci karo da taliar data dafa dazun saboda yunwa ma nan kitchen din yayi zaune ya cinye taliyar tas sanann yamike yadawo yashiga toilet yayi wanka yadauro alwalar ishai.saeda ya gama salalr tukuna yadawo kusa da zee ya kwanta wanda shima nan da nan barci yayi awon gaba dashi. Wajen karfe 3:30am mardiyya ta farka don yin fitsari,kallon inda muq ya saba kwancia a kasa tayi ta ga bashi ba alamar sa gabanta ya yanke ya fadi ya akai haka ta barshi ya tafi dakin zee dasauri tashiga tayi fitsarin daya matseta tareda nufar bangaren zeenatun murda kofar kawae tayi ta gansu kwance a kasa kusa da juna gaf gaf kishi yakara kama mardiyyar a fusace ta daka ma muq duka, kai !  Ubanwa ya baka izinin kazo dakin wannan abin kwana ?! Shiru yayi yana mutsitsika idanu wanda hayaniyar mardiyya yasa zee tashi dasauri tareda jawo innalillahi don ita ta zata ko wani abun ne yafaru, zuba ma mardiyyar ido tayi tana kallon wani sabon salon karfin hali, don haka mardiyya takalli zee tareda daka masu tsawa zaku min mgn kokuwa sae na ci uban yar iskar yarinyar nan ! Sosae ran zee ya baci ta bude baki zatay magana amma saeta sami kanta da kasawa kwata kwata kamar an jefa ma bakinta wani katon dutse, kasan zuciarta wani irin tafasa yakeyi saboda bacin rae amma babu halin mgn, bata san sanda ta sami kanta da cewa kiyi hkr antt mardiyya nima wlh bansan ya shigo ba, da sauri mardiyya ta kalle ta wani irin farin ciki ya cika mata zucia ganin tun kan garin ya waye aikinta yafara ci,yasa ta kara daure fuska takalli muq oya tashimun mutafi daki kuma daga yau sae yau wlh kada ka kuskura nasake ganin kafar ka ta tako dakin nan, suduf suduf ya tashi yabi bayan mardiyyar kamar wani danta yayinda aka bar zee zaune cikeda tashin hankali, hasbunallahu wani imal wakeel kawae ta fadi tareda tashi dakyar ta haye kan gadonta wanan wace rin maseefa ce anya kuwa zan iya zaman aure a gidan nan ko kwana daya banyi ba amma tashin hankalin cikin gidannan kamar ana yakin duniya.barcin dabae kara kama zee kenan ba a kunnenta akayi kiran assalatu don hka ta tashi ta dauro alwala tareda jero nafilfilinta data sabayi duk dare.
.

WACECE ITA?? Onde histórias criam vida. Descubra agora