Chapter 031: 💞 The sacred tie💞

827 79 0
                                    

💝Ni Nuwaylah💝💝
                   ☆☆na☆☆
  👑👑Bilqeessah Alpher 👑👑
   📚📚Marubuciyar 📚📚
   🖤🖤🖤BAKAR ZARGI🖤🖤🖤

✍Alpher's pen*
Bismillahir Rahmanirr Raheem

Bayan sallar maghrib ya kira ASK yace yanason ganinsa after Isha. Babu abinda bai kawo a zuciyarsa ba, daga baya ya hakura.
Ya shiga gidan kenan ya ma Nuwaylah text asking if it's okay ya kirata, daman through haka suke communicating, kullum in zai kirata sai ya notifying nata making sure bata cikin mutane to avoid suspicion.
Ta kirashi daman tana dakinta inda ta shiga wanka, suka dan taba hira, ya shaida mata cewa yana gidan and hope to see her.
Staright dakin mummy ya wuce, yayi sallama ta amsa masa maimakon ya karaso ciki ya tsaya a bakin kofa  ya sunkuyar da kai.
Ya tsuguna har kasa ya gaida ita, ta zuba masa ido for few seconds, sannan tace
"Babana lafiya? Ka wani tsaya a bakin kofa, kakaraso mana"
Ya mike tsaye yana tafiya kaman yanda kwai ya fashe a cikinsa, a gabanta ya zube yana bata hakuri. Ta sauko ta rungumeshi tana comforting dinsa
"It's okay, haka ƙaddara ke zuwa wani lokaci, it was ordained to happen and there is nothing we can do. Allah Ya kara kiyayemu Ya kuma bamu sa'an cin jarabawarmu"
Ya amsa da Ameen, wasu hawaye suka gangaro masa, yayi danasanin karyan da ya masu, at this point he wished he can just tell her the truth amma yasan bazai iyaba don in yayi hakan ba shakka zai rasa Nuwaylah.
Ta rike hannunsa tajashi dinning already an riga anyi setting abincin ko ta zaunar dashi, sai ga Yasmeen ta fito, a jikinsa ta fadi tana masa shagwaba as usual, shi kuma yana biye mata.
Daddy ya sauko shima ASK ya sauka har kasa ya gaida shi ba yabo ba fallasa ya amsa masa, bayan sun zauna duka mummy ta tura Yasmeen kiran Nuwaylah, after like 2 mins sai gasu sun dawo tare.
Ta durkusa har kasa ta gaidasu kaman yadda tagan Yasmeen keyi, tare Daddy da mummy suka amsa mata, ta ɗan juya gefen ASK ta gaidashi, ya amsata with few words with much meaning, wanda dagashi sai ita suka gane.
Yasmeen tayi serving nasu, tasa nata da na ASK a plate daya, Nuwaylah kallonsu take yanda suke cin abinci ke birgeta, she wished her family is still alive, wasu guntun hawaye masu zafi suka gangaro mata tasa hannu ta goge su kafin wani yagane.
Mummy wace idonta na gan ta ta gani, ta tausaya mata, she now understands why mijinta ya yanke shawarar haddasu aure. Son yarinyar ya kara shiga zuciyarta, tama kanta alkawarin riketa kamar nata diyar.
Bayan sun gama Daddy da ASK suka shiga office din Daddy. Daddy yamasa nasiha sosai sannan daga baya ya shaida masa hukuncin da ya yanke masu.
He was so shocked, he never expected things to be this easy, ya dan dago ya kalli daddy to be sure yanayin fuskarsa yasa ya gane da gaske yake. Wani irin farin ciki ya cikashi, ji yake kamar yayi tsalle ya taka rawa, da kyar yayi composing kansa so that Daddy bazai gane yanayin da yake ciki ba.
Daddy ya kalleshi yana studying mood nashi, he noticed he was a little bit disturbed amma yana kokarin boyewa. Daddy yace
"Although ba shawararka nake nema ba, amma zan baka daman fitar da yarinyar da kakeson aura, so that a daura maku aure, if possible kafin ta haihu or a daura rana daya da nata depending on how you want it."
ASK ya sosa keya yace
"Daman banda wace nake so yanzu, amma tunda ka yanke shawarar haddamu aure na amince, bazan taba jayayya da ku ba".
Maganarsa yayi ma Daddy dadi sosai, yayi murmushi yace
"Masha Allah, Allah yayi maka albarka, ya baka yaran da zasu maka biyayya. Yanzu itama Nuwaylah nasa mummynku ta mata bayani".
Da haka suka cigaba da tattaunawa.
Bangaren su Nuwaylah kuma, bayan sun gama cin abinci mummy tayi requesting ganinta, dan guntun wa'azi mummy ta fara mata sannan ta daura da cewa
"Inason ki sake jikinki da mu ki mayar damu kamar iyayenki, Inn Sha Allah muma zamu rikeki kamar diyar cikinmu. The main reason dayasa na kiraki is to inform you akan hukuncin da dadaynsu ya yanke".
Tayi shiru kadan tana kallonta sannan ta cigaba
"Ya yanke shawarar haddaku aure".
Dagowa tayi babu shiri tana kallon mummy, she was so shocked, how is that possible? Mummy bata bata forum da zatayi dogon tunani ba ta cigaba
"Truth be told banso auran nan ba at first, but I was convinced by their Dad, that's the best he can do to make you feel not neglected and cheated. In addition kuma nan da wata biyar Inn Sha Allah zaki zama uwa, no mother will want to part ways with her child and muma bazamu guji jinninmu ba, we can't throw her away simply because she was born under some ill-fated circumstance. The best we can do is to unite the parents, amma in hukuncin bai miki ba you are free to voice out your veiw".
Nuwaylah ta rasa abin cewa due to mixed reactions, despite the fact that tanason auran ASK domin shine babban burin ta a nan Nigeria she can't neglect the fact that she's cheating on them and taking advantage of their kind hearts.
Nan da nan hawaye suke gangaro mata ta fara kuka tace
"Ma I'm sorry, please forgive me, I'm sorry..."
Mummy ta taso ta rungumeta tana rarashinta, har ta hakura, ta tambayeta inta yarda da hukuncin ta daga mata kai. Murmushi mummy tayi tana Hamdallah.

Ni Nuwaylah A Hausa Love StoryWhere stories live. Discover now