BAYAN YAKIN UHUDU

19 7 2
                                    

Safiya bnt Abdulmuddalib yar uwar Hamza ibn Abdulmuddalib ce, labari kuma ya riga ya risketa cewa an kashe dan'uwa don haka ta taso don ganin gawar dan'uwanta shugaban shahidai Hamza (R.A). Annabi baya son taga gawar don kada hankalinta ya tashi saboda irin kisan da akaiwa dan'uwanta, don haka saiya umarci danta Zubair Bn Awwam daya hanata karasowa inda gawar Hamza take. Dan nata yayi maza ya tare ta ya gaya mata cewa Annabi  baya son taje don ganin wannan gawa. Budar bakinta ke da wuya sai tace "Saboda me? Ai nasan an yiwa dan'uwana kisan wulakanci, sai dai akan tafarkin Allah ne kuma ina burin Allah zai saka masa da mafificin alheri, ni kuma insha Allah zan zama mai hakuri." Daga nan taje taga Hamza tayi masa addu'a. Bayan nan Annabi yasa aka binneshi anan filin Uhud kabarinsa har yau yananan. 

Mus'ab wanda ya daukarwa musulmi tuta a wannan yaki na Uhudu, ya kasance mafi kwalliyar mutane a makkah, kafin musulunchi. Domin kuwa dai dai da turaransa ya fita dabam. Shima a wannan yaki na Uhudu aka kasheshi. Kuma dai dai da tufafin da aka binneshi dashi bai iya rufeshi gaba daya ba. 

A hanyar Annabi da Sahabbai ta komawa madina, sahabbai suka hango wata mata ta bazamo hankalinta a tashi... An gaya mata mijinta, babanta da dan'uwanta duk sun rasa rayuwarsu a filin daga. Abinda ta fara tambaya shine shin ina Annabi Muhammad (S.A.W)? Aka gaya mata yana raye.  Nan ta godewa Allah. Amma sai zuciyarta ta kasa samun nutsuwa. Sai tace to indai yana raye tana so a kaita wajenshi. Ai kuwa sai aka kaita. Sai tace tunda yana raye ai dukkanin kuncinta yanzu ya yaye. Damuwar data shiga saboda tunanin an kasheshi yanzu babu ita. 

Jama'a mu kula da kyau. An kashe mijinta, babanta da dan'uwanta. Amma ita Annabin dai shine abinda yafi damunta.

Tabbas sahabbai sun cancanci yabo da addu'a.

Ka duba irin wahalar da Sahabbai suka sha, da kuma irin raunukan da suka ji a wannan yaki, amma washe garin ranar Annabi ya sake bada umarnin a fita abi bayan kafirai. Haka sahabbai suka dunguma suka bi bayan kafirai. Dalilin wannan bin baya kuwa shine akwai yiwuwar kafiran zasu farwa madina. Domin burin da suka zo dashi shine suyiwa musulmi kaca-kaca su kuma shiga har madinan. Amma tun a farkon yaki da akaci galaba a kansu sai suka tsorata, tare da cewa bayan sabawa umarnin Annabi da sahabbai sukai sai kafirai suka samu karfi akansu bisa taimakon Khalid bn Walid. Musulmai suka shiga rude da tashin hankali daga bisani kuma suka sake hade kawunansu a waje daya. Don haka ganin musulmai sun sake hadewa sannan kuma da kiran da Abu Sufyan yayi yaji cewa lallai tabbas Annabin rahama da Abubakar da Umar duka suna raye shine ya sake jefa tsoro a cikin zukatansu inda suka kasa aiwatar da wani abu face ikirarin sake haduwa a wata shekarar a filin BADAR, suka kuma bar wannan yaki a matsayin fansar yakin badar ne, suka kuma yi da'awar cewa anyi kare jini biri jini da su da musulmai. Amma sai gwarazan musulunchi suka nuna musu akwai bambanci. Domin mamatan musulmai suna Aljanna, mamatan kafirai kuwa suna wuta.

Allah ne mafi sani.

A shekara ta uku bayan hijira wasu kabilu biyu suka turo wakilai cewar suna so Annabi ya hadasu da wasu daga sahabbansa don su koyar dasu addini. Annabi kuwa saiya basu mutum shida. A hanya sai kawai suka kame wayannan sahabbai zasu daddauresu. Wayannan sahabbai suka fito da makamai don kare kansu. Wayannan kafirai suka gayawa sahabbai cewa ba zasu kashe suba. Su kuwa uku daga sahabban suka ce ba zasu yarda da wannan abu daga kafirai ba. ai kuwa sai kafiran nan suka kashe su, suka tafi da ragowar ukun, a hanya suka sake kashe daya. Ragowar mutum biyun kuwa sai suka sai da su ga Kuraishawa. Hujair bn Abu Ihab ya sayi Khubaib bn Adiy (R.A), Safwan Bn Umayya kuma ya sayi Zaid bn Dasinna (R.A). Dukkaninsu sun siye su don daukar fansar yan'uwansu.    

Aka tara mutane don a makkah don suga irin kisan da za'a yiwa Zaid bn Dasinna. Kafin kisan suka tambayeshi shin yanzu baya burin ace Annabi aka kama ba shi ba, shi yana can wajen iyalansa? Sai yace musu. "Na rantse da Allah, bana burin kaya ta caki Annabi, alhalin ni ina cikin jin dadi nida iyalina."

Abu Sufyan yana wajen ya cika da mamaki, yace shi bai taba ganin mutumin da akewa irin wannan soyayya ba sai Manzon Allah.  Daga nan suka kashe zaidu. 

Shi kuwa Kubaib, da aka zo za'a kasheshi, sai ya nemi a barshi yayi sallah raka'a biyu. Ai kuwa sai suka barshi. Bayan ya idar sannan ya juyo ya kalli kafirai yace ba don kada kuyi zaton na tsawaita sallar don tsoron mutuwa ba da sainayi sallah mai yawa. 

Daga nan kafirai cikin rashin imani suka dauko wukake suna yankar naman jikinsa suna tambayarsa "Shin kana so a kama Annabi a maimakonka kai kuma a sake ka?" 

Jini na zuba radadi da zafin yanka yana ratsashi inda aka zabtari namansa yana zubar da jini amma a hakan cikin juriya da imani zai rinka bada amsa yana cewa "Wallahi bana burin in zauna lafiya alhalin kaya zata soki Annabi Muhammad..."

Haka suka rinka yankar naman jikinsa suna bijiro masa da wannan tambayar, shi kuma yana maimata musu wannan amsar a karshe har saida suka gaji suka karasa kasheshi, kafin ya mutu ya daga kansa sama yayi musu mummunar addu'a.

Ba zaka gane munin irin kisar da sukai masa ba sai kaji daga bakin wanda ya halarta.

Bari mu kawo daya daga cikinsu.

A wata ziyara da Sahabi Umar yakai garuruwan Sham lokacin kalifancinsa, ya shiga Himsa, sai mutanen garin suka kawo masa karar sarkinsu mai suna Sa'id bn Amir akan wasu abubuwa guda hudu. Laifin farko yafi na biyu...

Sai Umar yasa aka kirawo sarkin alhalin suma suna nan zaune, saiya tambayesu me kuke kokawa akan sarkinsu.

Suka ce: Baya fito mana har sai rana ta dago.

Umar yace da shi, me zaka ce akan haka?

Sai Sarki sa'eed (R.A) yayi shiru, daga bisani yace: Bana son fada wallahi, sai dai babu makawa saina fada. Iyalina basu da dan aiki, ni nake tashe na nika musu garinsu, sannan in kwabashi sannan inyi musu gurasa, sai inyi alwala in fita inyi sallah.

(Ina maza masu kin taya mata aiki, to ga abin koyi).

Sai Umar yace: Sai kuma me kuke kawo kara akansa?

Sukace: Baya amsa kiran kowa da daddare.

Umar ya sake cewa: To kai Sa'id me za kace?

Sai Sarki Sa'id yace: Wallahi wannan ma bana son fada... Ni na sanya rana garesu da bukatunsu. Dare kuma na barwa Allah ina bauta masa.

Sai Umar (R.A) ya kuma cewa: Sai kuma me kuke kawo kara akansa.

Sai suka ce: A wata, akwai wata rana guda da baya fitowa garemu baki daya.

Sai Umar ya tambayeshi dalili.

Sai Sarki Sa'id yace: Bani da mai yi mini hidima, kuma bani da wani kayan bayan wanda ke jikina, saboda haka ina wankeshi sau daya a wata, sannan in jira har sai ya bushe don haka bana fitowa gare su sai yamma likis.

Sai Khalifa Umar ya sake tambayarsu sai kuma wacce matsala.

Sai suka ce: Wani abu mai kama da Suma ko farfadiya, saiya fita daga hayyacinsa baya sanin wake tare dashi ko a ina yake. don haka saiya boya ga wayanda ke wajen zamansa...

Sai Umar ya tambayeshi dalili.

Sai yace: NA HALARCI KISAN DA AKAIWA KUBAIB IBN ADIY LOKACIN INA MUSHRIKI, QURAISHAWA SUNA YANKAR NAMAN JIKINSA SUNA TAMBAYARSA...(irin tambayar da muka fada a baya)... HAKIKA NI BANA TUNA WANNAN RANAR, DA KUMA KIN TAIMAKONSA DA NAYI FACE NAYI ZATON ALLAH BAZAI TABA GAFARTA MIN BA... SHINE NAKE WANNAN SUMAN.

Ka duba fa, yana kafiri abin ya faru, amma har bayan ya musulunta idan ya tuno saiya suma kai kuwa wannan wacce irin kisa akayi?

Bayan wayannan wasu mutanen suka kuma zuwa suka nuna sha'awarsu ga musulunchi, suka nemi a basu malamai su koyar dasu, Annabi ya zabi mutum saba'in ya hadasu dasu. Suka tafi dasu da sukazo wani guri mai suna Bi'r Ma'una kabilar Banu Sulaym, Usayya, Ri'il da Zakhwan sai sukaiwa musulman nan rubdugu. Jarumta Musulman suka rinka kare kansu a karshe aka kashesu kakaf, Ka'ab Bn zaid ne kawai ya tsira ya dawo ya bada labari.

Zamu tsaya anan

Sai kuma a rubutu na gaba! 

Naseeb Auwal
Abu Umar Alkanawy!

TARIHIN ANNABI MUHAMMAD (S.A.W)Où les histoires vivent. Découvrez maintenant