Chapter 11

25 0 0
                                    

🏵️ NACINA YAJAWOMIN🏵️
                          

Narrnarhh Bukar✍️

🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
  ✨ P. E. W. A✨

Masu telegram zaku iya following ɗina acan🤗🌹👇👇👇
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk


Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:@Narrnarhh002



🌹🌹🌹I'm  not born to be a writer but born to be a great professional writer✍️✍️✍️🙃🙃🙃🌹🌹🌹

🤗🤗🤗Special greetings to y'll my Esteem fans,i love y'll💝💝💝💝🤗🤗🤗



2⃣1⃣----2⃣2⃣


"Kwantar da hankalinki duk wannan kururuwan da kike bashi bane bafita Ƙawas"

"To mai kike so inyi bayan hankalin Babansu Nusaiba ya fara karka garesu, wallahi nasan kashina ya bushe idan na bari hankalinsa ya koma kansu"

"Haba don Allah nace ki kwantar da hankalinki ko,zamu samu mafita akan wannan lamarin,ke bari ma kiji akwai mafita amma mafitar ɗaya ce garemu yanzu "

"Akwai mafita kika ce Maman Jummalo,to mecece mafitar? "

"Ba wata mafita bace illa mu shiya ranar lahadi muje wurin boka Sankeru,ita kadai ce mafitar tamu kinga sai ya duba yaga ko asirin ne ya warware"

"Haka ne kuma,kin kawo shawara mai kyau amma anya zan iya bari har lahadi Ƙawas,lahadi tayimin nisa ji nake kamar yanzu na ganni gaban boka Sankeru,ko hankalina zai kwanta"

"Haba Saratu,kin cika gaggawa a al'amuranki wallahi ina nan ina ranar lahadi,kin manta yau alhamis baifi saura kwana biyu ba amma duk kin bi kin tada hankalinki a banza,haba don Allah"

"Allah ya kaimu ɗin"

A haka Maman Jummalo ta cigaba da kwantar ma Umma Kande hankali har ta natsu,sai daga baya ta wuce ɗakinta ,sallar subh ma da  ta ce zatayi tafasa sai bayan ta dawo daga wurin boka Sankeru zata cigaba da sallah.(Ohhhh niii!!! Duniya ina zaki damu🤔🤔🤔,wannan wani irin jahilci ne haka,kai! Kai!! Kai!!!,to Allah ya kyauta🤔🤔🤔).

Haka duk wunin ranar jikinta a sanyaye yake,abinci ma sai da Maman Jummalo ta lallabata sannan ta samu taci shima kaɗan,duk tayi sukuku da ita kamar mai ciwo ko kuma ance  wani shaƙiƙinta ya rasu haka take ji a jikinta.

                    @@@@@@

Bayan su Sa'eeda sun fito waje sai ta dubi Ummanta tace

"Ummina kinga ikon Allah ko"

"Haka ne sanyin idaniyata,tabbas wannan  ikon Allah ne ba na mutum ba,amma a gaskiya nayi mamakin sauyawan Abbanki lokaci guda haka"

"Nima haka Ummina,Allah shi ne abin godiya"

"Haka ne kuwa Allah shi ne abin godiya, don ba yin mu bane,nufin Allah ne"

"Hakane Ummina,kinga kuɗin nan da ya bani saina ƙara kuɗin mota sannan zanyi sadakar naira dubu ɗaya wa almajirai ko ya kika ce Ummina"

"Wannan haka yake,Allah dai ya cigaba da maido da hankalinsa gare mu"

"Aameen Aameen Ummina"

Haka suka cigaba da hira har  kowa ya nufi hanyarsa.

                @@@@@@@@

Cigarta aji keda wuya saiga Maryam itama ta shigo,murmushi Sa'eeda ta sakarma Maryam sai itama ta maido mata da ɗan murmushi wanda bai kai zuciya ba, babu yabo babu fallasa a fuskar Maryam ta gaida Sa'eeda don yanzu Maryam ta fara jan baya baya da Sa'eeda dalilin samun ƙawaye ƴan gayu masu ji da kuɗi tare da class da tayi.

NACINA YA JAWO MINWhere stories live. Discover now