Chapter 34

35 1 0
                                    

🏵️ *NACINA YA JAWO MIN* 🏵️


*Narrnarhh Bukar*
( *The Amazing Pen* ✍️)

*TASKIRA WRITER'S FORUM*
*T.W.F*

*WATTPAD*
https://www.wattpad.com/user/AISHAABUBAKAR812?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

*AREWABOOK*
https://arewabooks.com/book?=6615ba31404e6e2687888ab9

*TELEGRAM*
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk

*WHATSAPP CHANNEL*
https://whatsapp.com/channel/0029VaRTjCw8vd1HiLjaNK2y

*BOOK 2*

*Second to the last pages🙃🙃🙃*

6⃣7⃣----6⃣8⃣

Ɗan murmushi tayi sannan ta  ce

"Wata shawara ce nazo da ita kuma ina fatan zata karɓu  a gareka,ganin Umma Kande a irin wannan hali,gashi su Iklima sun kusa aure,ita ma Nusaiba muna mata fata samun miji a nan kusa tayi auran ita ma,shi ne nace mai zai hana ka auri Maman Jummalo domin idan yaran sukayi aure gidan watsewa zaiyi,ya zama babu kowa don kasan Maman Jummalo da wuya ta cigaba da zama a gidan,kaga idan ka aureta zata cigaba da kula da Umma Kande sannan yaranka zasu samu madogara tunda ni ba'a gidan nake ba yanzu,kuma yaran sun ɗauki Maman Jummalo a matsayin mamansu,a tunanina hakan zaifi dacewa"

Shiru yayi yana kallonta ko ƙifta idanunsa baya yi,sai can ya sauke goron ajiyar zuciya sannan ya ce

"Kenan bakya kishina Hussaina"

"Haba ina kishinka sosai ma kuwa,saidai duk abinda mutum zaiyi a rayuwa dole idan zaiyi *sara ya dinga duban gatari* ,taimako ne zamuyi Sulaiman na farko mun ƙara inganta rayuwar Maman Jummalo saboda aure shi ne cikar martabar ɗiya mace sannan bazata koma kauye ba,kaga tana buƙatar aure tunda ba tsufa tayi ba sannan zata kular matlka da matarka sosai saboda aminiyarta ce,kaima karan kanka zakaji daɗin ganin ana kula maka da matarka haɗi da yaranka idan hidimar hakan ta taso tunda ni ba gidan nake ba,da ace a gidan nake da wallahi bazan kawo shawarar ka aure Maman Jummalo ba saboda ina matuƙar kishinka amma yanzu babu maganar kishi tunda ba gida daya muke ba"

Shiru tayi yana kallonta sai can ya ce

"Hussaina kinzo min da magana mai girma wacca ƙwaƙwalwata ta kasa ɗauka,zanyi shawara tukunna idan da hali  ƙila na amince,idan kuma zuciyata taƙi yarda wallahi komai zakiyi bazan amince ba,to wai da kike cewa na auri Maman Jummalo, idan kuma taƙi amincewa fa"

"In Shaa Allah zakama amince itama haka zata amince angon Hafsy"

Tana maganar tana dariya

"Au! zolayata ma kike Hussaina,ya miki kyau"

"Ni na isa na zolayi gwarzon namiji kamarka,wace ni Hussaina"

Dariya shima yayi ba tare da ya bata amsa ba suka cigaba da kallonsu.Bayan kwana biyu yayi shawara sai ya amince itama Maman Jummalo ta amince,nan da nan maganar aure yayi ƙarfi har ƙauyensu Maman Jummalo Abban Sa'eeda yaje,ba tare da ɓata lokaci ba aka daura musu aure a can tunda har sadaki ya biya,su Nusaiba da Iklima sunyi murna sosai da wannan auran.

A ɗakin Umma Kande ta tare bayan an cire komai na ɗakin tare  da ƙara gyarashi haɗi da sabon fenti,kayanta ta dawo dasu ɗakin Umma Kande, saida suka sha amarci har na tsawan kwana uku sannan suka raba kwana bayan yakai Maman Jummalo gidan Umman Sa'eeda wanda yanzu har da mota garesa wanda sirikinsa Sadam ya siya masa,Sa'eeda ma tayi murna sosai duk da kishiya aka ma Ummanta amma dai koba komai Maman Jummalo zata kula da tarbiyyar su Nusaiba kamar wacca ta haifesu sannan zata kula da Umma Kande idan yaran sunyi aure kasancewsar auransu baifi wata uku ba.

NACINA YA JAWO MINOpowieści tętniące życiem. Odkryj je teraz