Chapter 27

37 0 0
                                    

🏵️ *NACINA YA JAWO MIN* 🏵️




*Narrnarhh Bukar*
( *The Amazing Pen* ✍️)


*TASKIRA WRITER'S FORUM*
*T.W.F*


*WATTPAD*
https://www.wattpad.com/user/AISHAABUBAKAR812?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends


*AREWABOOK*
https://arewabooks.com/book?id=6615ba31404e6e2687888ab9


*TELEGRAM*
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk

*WHATSAPP CHANNEL*
https://whatsapp.com/channel/0029VaRTjCw8vd1HiLjaNK2y

*BOOK 2*

5⃣3⃣----5⃣4⃣


A cikin labour room ɗin nurses uku ne suke taimaka mata wurin amsar haihuwan wanda Maman Jummalo tasha baƙar wahala kafin ta haihu,nurse ɗin da take a wurin da yaro ya fito hankalinta yayi matuƙar tashi jin *kukan jaki* to a ina haka? Mamaki ne ya cika sosai, to a ina aka samu jaki ne haka,sai kuma wata daga cikin nurses ɗin wacca take kusa da ita  ta ƙwalla abun  ƙara tana nuna wurin da yaro ya faɗo,ai da sauri wacca taji kukan jakin takai dubanta ga wurin,ita ma ƙwalla ƙarar tayi ganin jariri da *kan jaki* amma sassan jikinsa na mutum,ikon Allah haka nurses ɗin suka tsaya suna kallon yadda yake kukan jaki amma an kasa samun wacca zata ɗaukeshi don a goge mishi jiki,ji kake yana

"Hiiiihiiiiih!!! Hiiiiihiiiiih!!! Hiiiihiiiiih!!! "

Ita kuma Maman Jummalo an koma baccin gajiya,a nan wata daga cikin nurses ɗin tayi shahadar ɗaukansa don a goge masa jiki,jikinsa irin na mutane amma kansa exactly na jaki,ga ƙwayar idanunsa idan ya ɗan buɗesu kalar na maguna ne,haka nurses ɗin suna tsoro-tsoro haka suka goge mishi jiki da Olive oil,sannan aka saka mishi kayan da suka amsa wurinsu Umma Kande daman da kayan haihuwa suka zo asibitin,wata a cikin nurses ɗin ta ciro wayarta tare da ɗaukar hotunan jaririn ta ɗora a social media,ai kan kace me hotunan jaririn Maman Jummalo sun karaɗe social media.Bayan an shirya jaririn sai wata nurse ta fito dashi a lokacin yayi bacci tare da miƙa ma Umma Kande kasancewar tafi kusa da ƙofar labour room,da sauri da amsa yaran tana farin cikin amma me tana tozali da kan yaron ƙirjinta ya bada Ras! Cikin rawar murya Umma Kande ta ce

"Innalillahi wa'inna ilaihi Raji'ana!!! Ni Sarere jikar Sarkin ruwa mi zangani haka yaro da kan jaki!!! Kai kuzo su Auta kuga abinda na gani"

Still jikinta na ɗaukar ɗan mazari haka take maganar,su Jummalo da Iklima da sauri suka matso inda take tare da kai dubansu ga yaron,ai kamar haɗin baki haka suka furta

"Inna'illahi Wa'inna Ilaihi Raji'un!!! "

Jummalo ce ta cigaba da magana cike da tashin hankali

"Mun shifa uku mun lalace ɗa mai kan jaki mama ta haifa!!! Ya Salam!!! Tamu ta samemu!!! Wayyo Allah ni Jummalo!!!....."

Kuka take riris tana ƙara duba yaron da kyau kodai idanunta ne basu gani da kyau ba,tabbas mai kan jakin mamanta ta haifa,zuwa wurin boka ya musu riba,kuka take sosai ita kuma Iklima tana lallashinta akan tayi shiru kar mutane su san meke faruwa su taru a wurinsu,ita kuma Umma Kande ƙara kallon yaron take sosai shi kuma bai san ma mai ake ba,baccinsa yake hankali kwance tunda sanda ya fito daga mahaifar uwarsa tare da tsandara kuka irin na jaki bai kuma kuka ba har goge mishi jikin da ake duk yana ta baccinsa.

Nurses ɗin da suka amshi haihuwar ne wata a cikinsu ta cema sauran nurses din da suka tsaya sunyi cirko-cirko suna kallon su Umma Kande da yaron sun ƙi tafiya

"To ya za'ayi da Mom ɗinsa,bacci take kuma ya kamata akaita ɗakin hutu"

"Kuma fa hakane,muje mu kaita ɗakin hutu tunda gadon mai taya ne,abun yazo da sauƙi" cewar wata nurse

NACINA YA JAWO MINWhere stories live. Discover now