🥀🥀🥀 *RAYUWAR AURENA*🥀🥀🥀 *NA* *HAFSAT M* *Page*

1.2K 57 0
                                    

🥀🥀🥀 *RAYUWAR AURENA*🥀🥀🥀

        *NA*

*HAFSAT M*

*Page*

        *59*

Sadaukarwa ga qawata
*AISHA GENTLE LADY*




Yi haquri hajiya ai bangane ki bane shiyasa kikaga ban baki hanya ba" Haushi maganar tasa yabata cike da takaici tace Haba malam musa ni Humairan ne zakace baka gane ni ba kodai kawai neman magana kake"?

  "Allahu akbar ya salam ranki ya daďe ki gafarce ni wlh fuskar takice ta canza min wani iri shiyasa bangane ki ba, bisimillah ga hanya ki shigo kawo jakar taki, Cike da rusunawa yake mata maganar yabata hanya dan ta wuce yana miqa mata hannu dan ya karbì bacgon dake hannunta, fuskan sa cike da mamaki yana tambayar zuciyar sa to meye yasamu hajiya humaira haka ta lalace tamkar ba yar gata ba."

"Batareda ta kuma bi ta kansa ba tasa kai cikin gidan tana faďin bar min kayana zan iya shiga dashi basai ka karbà ba kuma kada kasanar da Abba ina gida idan yadawo" Kai ya girgiza mata ba musu ta shige abunta, yana tsaye yana binta da kallon al'ajabi ta baya domin shi ganin ta cikin irin wannan yanayin ba qaramin mamaki ya jefa shi ba dan ko amafarki akace masa wannan humaira ce ta koma haka dakyar zai yarda bare yanzu azahiri."

"Da yake cikin gidan nasu babban gida ne yana ďauke da babban fili, An mamaye shi da flawers masu kyawun gaske ya sanya gidan yin bala'in kyau da tsari."

  "Tana cikin tafiyar ne tadawo da baya zuwa inda malam musa ke tsaye yana riqe da habàr sa har zuwa lokacin idanunsa yana kanta, Ganin ta dawo inda yake ne yasa ya maido da hankalin sa gareta, Cikin qasa da murya tace Suwaye da waye ne agida, Abba yana nan"?

"Kai ya girgiza mata alaman a a kafin yace, Abban ki dai baya nan bai dawo ba Amman nasan duk yanda akayi yanzu yana hanya yayanki kuma gaskiya shikam zuwan sa zai iya kaiwa dare Amman dai Hajiya tana ciki ba inda taje....
   "Kai ta kaďa ta shige cikin gidan batareda tsaya ciki gaba da sauraran tambayar da tayi masa ba dan ganin bàta mata lokaci yakeyi daga tambaya ďaya da tayi masa yakama jero mata bayanai."

"A hankali take taka ķafar ta tamkar kace marar gaskiya tana tafiya tana waige waige, cikin zuciyar ta tana fatan Allah yasa tashiga ciki kai tsaye har ďakinta batareda Mummy ta kalleta ba."
    "Tana dafda shiga cikin parloun nasu tajiyo motsi daga kitchen alamun ana tabà plates" Zuciyar tane sosai yafaďi sakamakon ďaga kai da tayi ta hango Mummy tsaye kusa da gas ta juya bayan ta da yake window kitchen ďin babba ne yasa ta iya hango ta sosai."

  "Numfasawa tayi a hankali ganin alamun hankalin Mummyn yana kan aikin da take ya sanya tasa hannu ajikin ķofar parloun a hankali ta buďe ta shiga."

"Cike da sauri ta haura saman beni ta nufi ďakin ta batareda tsaya bàta lokaci ba  tana fata a ranta Allah yasa ķofar a buďe take basu kulle ba tunda yanzu bata gidan domin a nan take ganin zatafi sakewa har tagaba shirin ta batareda wani ya shigo ya ganta ba."

  "Hamdala tayi a ranta tana murmushin jin daďi sanadiyar samun ķofar da tayi a bude" kutsa kai tayi ta shiga tareda mayar da ķofar ta rufe tasa masa key ta ciki kafin ta qarara bakin gado ta zauna tanabin cikin ďakin da kallo, Sosai taga ya canza mata tamkar ba shiba ga wani irin ni'imataccan ķàmshin turaren wuta dake tashi a ciki tareda sanyi sanyi mai ratsa kankan jiki."

  "Ajiyan zuciya ta sauķe tareda buzar da iska ta bakinta, cikin wani irin farin ciki ta kwanta rigingine akan gadon tana lumshe idanunta fuskan ta ďauke da lautsatstsar murmushi najin daďi a ranta tana faďin ohh finally now i have came back to my home thank u ya rabbi...

RAYUWAR AURENA Where stories live. Discover now