Page 1

4.6K 215 5
                                    

'☆'-'☆'-

☆"˜•☆•

¸☆"☆ª☆_☾'☆•
❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠

*TANTIRANCI KO KARUWANCI*☆
*.¸¸.*♠ *.¸¸*❆ ¸¸.*🤱🏻¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆
'☆'-'☆'-

☆"˜•☆•

¸☆"☆ª☆_☾'☆•
{Fad'i alkairi ko kayi shuru)🤫
A true life story
*Follow me on Wattpad @rahamanalele*

Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆

https://www.facebook.com/groups/354329565057948/
" بسم الله الرحمن الرحيم
Page 1

Matar Aure ce na yarjema ta karanta wannan labari nawa, Sannan ki d'auki abu me amfani kibar bara amfani, ban yarda kina budurwa ko bazawara ko kana saurayi ko bazawari ku karanta min labari ba..

Waige waige yakeyi acikin layin nasu. Sam bazai wacce shekaru ashirin da biyar ba. Yaro ne kyakkyawa ajin farko wanda kallo d'aya zaka mai kasan ya had'u tako ta'ina.
Ya tara abubuwa kamar haka..Tantiranci. Wayewar zamana. Ilimi. Iya wanka...
ABDUL D'AN KASADA kenan me karatu...
Abokansa ne suka sakamai wannan sunan ashekara biyu kad'al kuma ya bishi..

ABDUL ya rasa abubuwa uku arayuwarsa..
Ya rasa soyayyar Mahaifiyarsa da y'an uwansa.
Sam mahaifiyarsa Mama Saude bata qaunarsa arayuwarta. Bata da abun qi kamarsa a rayuwa.
Tunda ABDUL ya tashi bai tab'a ganin ranar daya zauna shida ita sukayi magana irinta uwa da d'a ba.
Kullum cikin cikin hantaransa take da nuna masa tsana. Kai baqin hali dai iri iri ba wanda ABDUL baya gani agun Mahaifiyar tasa..
Kaf cikin gidansu da unguwarsu ba wanda baisan da zaman qiyayyar da Mahaifiyar tasa take masa ba. Hatta abokansa suna mamakin irin tsanar da Mahaifiyar tasa take masa.
ABDUL yana da aboki AMEER.
AMEER layinsu d'aya da ABDUL
Saidai AMEER iyayansa masu kud'in gaske ne. Sam bazaka tab'a had'a gidansu AMEER danasu ABDUL ba.
Saboda gidansu ABDUL shine gidan talakawa na biyar acikin unguwar tasu.

AMEER tun tasowarsa arayuwa yake da rashin ji. Sam AMEER baya ganin kowa da gashi.
Ya rigada yayi suna wajen rashin mutunci..
Ga satan kud'in iyayensa da shaye shayen tsiya dabin mata kamar d'an akuya.
Sam bazakiso had'a Y'arki aure da AMEER ba..
Gashi su biyu kacal iyayensu suka Haifa shida qanwarsa Abida.
Suna sansu suna qaunarsu shiyasa yake amfani da Wannan damar yake iskancin dayaga dama..

Azahirin Gaskiya iyayensa suna matuƙar qoqari kan ya kintsu..
Dan basu san halaiyarsa kaf. Dan ko kad'an baiyiyo halinsu ba
Kasancewarsu nagari. Kawai sun yarda bata yanda Allah baya jarabtar bawansa.
Hakan yasa suke mai addu'a babu dare Babu ranah

Bambancin rashin jin AMEER da ABDUL abu biyu ne
Sam shi ABDUL baya bin mata baya aikata zina.. Sannan idan abinka zaikai shekara agaban ABDUL bazai tab'a d'aukar maka shi ba. Ma'ana anan baya sata baya aikata zina.
Saidai fa duk rashin mutuncin AMEER ABDUL yafishi. Dan shi idan yace yes baya dawowa yace no
Idan yace saiya aikata abu to Wallahi saiya aikata kodako abin nan zai kaisa ga caji office ne.
Sam ABDUL bashi da tsoro.

Gidansu ABDUL gidan yawa ne gidane irin gidan family house d'innan
Akwalla ba akasara ba yawan mutanan gidan zasukai su d'ari..
Gidan babban gida ne wanda yayi suna acikin unguwar. Suna kiran gidan da GIDAN YAWA. Saboda tsabar yawansu..

Alhaji Ali me katifa shike da mallakin gidan.
Yana da yara Ashirin da d'aya aduniya dukkansu maza.
Kuma kaf d'insu sunyi aure kuma agidan suke zaune da matansu da yaransu. Kasancewar gidan babban gida kowa idan yatashi auransa yankan wani shashi yake anan cikin gidan ya gina ya zauna da iyalinsa...

Mama Saude Ƴa ce ga qanwar Alhaji Ali yar autarsu. Amma ta rasu shekarun baya da suka wucce wajen haihuwan qanwar Mama Sauden wato ZAINAB.

Toh tunkan Mahaifiyar tata tarasu Alhaji Ali yake san Y'a mace kasancewar duk yaransa Ashirin da d'ayan nan duk maza ne.
Hakan yasa ya d'auki Saude tun tana qarama ya kawota gabansa wajen matarsa Hajjiya Ladi wacce kaf y'an gidan suke kiranta da Hajjiya Kakah.
Ita ta raineta har takai munzalin aure. sai alhaji Alin ya Aurar da ita ga d'ansa Shehu..
Shine suke zaune suma agidan har tasamu cikin ABDUL ta haifesa wanda tunda ta haifesa take nuna masa tsana dan qiri qiri qin shayar dashi tayi. Wai nononta nayi mata ciwo idan takai masa nonon bakinsa jitake kamar kan nononta zai gutsire.. Jin hakan sai Hajjiya Kakah ta d'auki ABDUL tashayar dashi da madara irin ta yara kamarsa awannan lokacin..
Kowa agidan Gani yake anya kuwa Saude itace ta haifi ABDUL.
Saboda sunga yanda take nuna mai tsana da tsangwama kala kala..

HALIN WASU MUTANAN Where stories live. Discover now