Page 24

2.6K 129 23
                                    

'☆´-'☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾'☆•
❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*🙆🏻‍♂*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠  
☆ *TANTIRANCI KO KARUWANCI*☆
*.¸¸.*♠ *.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*🙆🏼‍♀*.¸¸*❆
'☆´-'☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾'☆•🤱🏻
{Fad'i alkairi ko kayi shuru)🤫
      A true life story
*Follow me on Wattpad @rahamanalele*

Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆

https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R

” بسم الله الرحمن الرحيم
Page 24..

*😄😄😄😄 ina qaunarku MASOYA na*
16 read more nayi muku


*****************************
Kowane me rai dole yasan akwai ranar mutuwarsa, ZAINAB dai tatafi kuma bazata dawo ba, ABDUL bai tab'a tunanin yana San ZAINAB sosai haka ba, sanda ta rasu sannan ya San baqaramin So yake mata ba...
Toh ya zaiyi kowa zaman jiran tasa yake.

Hajjiya Kakah mama Saude Baban ABDUL ada Dady & Momy yan uwan arziqi, qawayen arziqi, masu saka ido marasa saka ido duk sunyi kukan rashin ZAINAB, dan ZAINAB mutum ce, kowa addu'ar Samar mata rahama yake..

Momy ce ta d'auki little Raheemat dan bata kulawar data dace..

Anyi uku anyi bakwai anyi arba'in, yanzu zaman kewa ake.

Kwanar goma dayin arba'in d'in ZAINAB ciwan daquda ya kama RAHMA..
Dake cikin dare ne ya tasar mata kusan qarfe d'aya, hakan yasa ABDUL Cikin tsoro matuqa, musamman kukan da RAHMAN take tana cewa, "ABDUL zan mutu, ABDUL zan mutu, dan Allah katemakeni, Yace "bazaki mutu ba my dear, idan kika mutu nima fa binki zanyi, ta qanqamesa tana sakar salati.. Ai ba shiri ABDUL yayi asibiti da ita, duk zuciyarsa a jagule take, yanzu idan itama ta mutu ya zaiyi😭😭..

Alwala ya d'auro a asibitin ya hau sallar nafula yana rokwan Allah ya saukarmai da ita lafiya, Sannan yabar mai ita surayu cikin inuwa d'aya..😭

Azaba kam RAHMA tashata, dan ba ita tasamu kanta ba sai kusan qarfe biyar na asuba, ta haifo kyakkyawan d'anta namiji, kallo d'aya zaka mai kasan ABDUL ne, dan kamar tasu tayi yawa kamar am tsaga kara.

Ma'aikatan asibitin na gayama ABDUL ta haihu tasamu d'a namiji yanzu haka tana d'akin Hutu ba qaramar ajiyar zuciya ABDUL yasake ba..

Yaje ya kama hannunta ya sumbata yace "Gashi dai baki mutu ba my
Baby, tayi mai murmushi tace, "Gaskiya Allah ya sakama iyayenmu da alkairi, wallahi sha kallo, haihuwa da zafi matuƙa, da gaske ji nake kamar bazan rayu ba, gaskiya bazan qara yin ciki ba, ta kai qarshen zancen nata da shagwaɓa..

ABDUL yayi murmushi da faɗin, "Ai yanzu kika fara my Baby, me akayi da maza, tunda Aunty Zainab bata nan, wannan alƙawari ne sai kin bani yara goma sha hud'u, little Raheemat tazama ta sha biyar..
RAHMA ta waro ido, tace "14 Babys..
Yace "Yeah, sunyi kad'an ne, tace "Yawa dai, ina ma lefin kaqara samun biyu nan gama, kaga 4 ai sun ishemu..
Yace "Ina, Wallahi da gaske nake miki yara goma sha biyar nake fatan Allah ya bani..

RAHMA tayi shuru tana tuno azabar data sha..
Saidai gashi ganin d'an nata ya wanke mata zafin fitowar tasa da taji..
ABDUL kamar ya cinye yaran nasa haka yake ji aransa dan qauna, yaran yazo da kyau ba lefi..
ABDUL ya kalli RAHMA da katse mata tunanin nata yace, "Wato duk girman wannan Cikin naki dama 1 zaki bani,
RAHMA tayi murmushi da cewa, "Toba gashi na baka kyakkyawa ba, me kamarka fa sak na haifo maka.
"Haka ne my dear, nagodema Allah Sosai daya bani shi, Allah ya qara sawa kibani Baby girl nan da 1 year..
RAHMA tayi shuru, yaci gaba da cewa, kinqi cewa komai, tace "Toh mezance..
Yace "kice ameen kawai, idan kuma kikaqi cewa sainayima kaina addu'ar Allah ya bani damar qara Aure nan da wata uku...
RAHMA ta kallesa da sauri, tare da wurga masa harara, tace, "me kace, da sauri ya rufe bakinsa da hannu yana girgiza mata kai alamar baice komai ba.
Cikin shagwaɓa taci gaba da cewa, "idan akan haihuwa ne zaka min kishiya, insha Allah bazaka tab'a yimin ba, ayanzu na cire tsoronta Allah yata bani ko ashirin ne zan baka mijina..
Ya shafa gefan fuskarta yace, "Yauwa nagode nutsuwata...

You've reached the end of published parts.

⏰ Last updated: Nov 14, 2018 ⏰

Add this story to your Library to get notified about new parts!

HALIN WASU MUTANAN Where stories live. Discover now