Page 4

1.2K 90 1
                                    

'☆´-'☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾'☆•
❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*🙆🏻‍♂*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠  
☆ *TANTIRANCI KO KARUWANCI*☆
*.¸¸.*♠ *.¸¸*❆ ¸¸.*🙆🏼‍♀¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆
'☆´-'☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾'☆•🤱🏻
{Fad'i alkairi ko kayi shuru)🤫
      A true life story
*Follow me on Wattpad @rahamanalele*

Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆

https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R

” بسم الله الرحمن الرحيم
Page 4

Dadyn yace "Nidai yanxu koma miye kuyi hakuri. Yaran yanxu ne mun haifesu bamu haifi halinsu ba. Kuduba AMEER d'ana kuga duk danginmu ba'a tab'a yin TANTIRI kamarsa ba, ko labari banjiyo irin hakan ba, kowa yasan da zaman hali irin nawa dana mahaifiyarsa sam bai yiyo halin d'aya daga cikinmu ba, to kunga ai dole sai munayi muna kai zuciyarmu nesa, dan haka dan Allah kubani bellin ABDUL kamar yanda kuka saba,
"Zamu baka belinsa Alhaji kamar yanda muka saba baka dan mutuncinka da kuke gani, amma dan Allah kudinga qara jamusu kunne dan ba abu bane me kyau ace kullum kaine wajen y'an sanda. Yanxu zaka iya bamu dubu Hamsin, DPO ya fad'i hakan da tsaida Kallansa ga Dadyn AMEER d'in.
Shuru Dadyn AMEER yayi, can yace zan iya baku indai zaku bani shi.
Nan suka bashi takadda ya cike ya basu kud'in sannan suka sako ABDUL.

Dadyn yana tuqin motar tasa yana kallan ABDUL lokaci lokaci, Can dai ya faka motar tashi kan hanya ya tsaida kallan nasa kan Abdul d'in yace.. "Na rasa dalilin dayasa nake jin qaunarka cikin raina fiye da AMEER, ina sanka ABDUL sosai cikin raina, yauma bata canja zani ba zan wara rokwanka a karon babu adadi kan kagyara rayuwarka kozaka iya gyaramin rayuwar d'ana, hak'ik'a ina rokwan Allah kan ya kintsar daku amma nasan yana jina kuma lokaci ya bani nasan zai kintsar daku. Kasani nasani AMEER bayajin maganar kowa sai taka, idan mukace mai gashi baya kalla amma idan kai kace mai gashi yana kalla, nasani Allah ne ya d'oraka akansa dan ban tab'a ganin wanda AMEER yake so kamarka ba, da wannan nake rokwanka daka kintsu ko shima zai kintsu, AMEER yafika aikata abubuwan ashsha nasani' dan ina kallo ina kuma ji ana kawomin qara,  kai idan ka aika tsiya kana dawowa kayi nadama kayi dana sani, amma AMEER bayijin komai bare yayi nadama, kai Yaro ne kin tsattse wanda kazama abin kwatance kaf faɗin unguwar nan tamu, hankalina ya tashi matuqa danaga ka tab'arb'are lokaci d'aya, dan Allah ABDUL ka dawo da rayuwarka kamar tada dan nasamu yanda nake wajen d'ana.

Kallansa ABDUL yayi cikin jin tausayinsa hak'ik'a yana jin tausayin dattijan aransa yana san shi yana qaunarsa kamar yanda yake jin mahaifinsa aransa da kakarsa da kuma AUNTYNSA ZAINAB.

"Kaci gaba dayi mana addu'a Dady insha Allah zan gyara rayuwata albarkacin addu'ar da kuke mana, Wallahi bana jin dad'i abubuwan da muke aikatawa, na kanyi nadama ayayin dana aikata, Dady har kuka nakeyi cikin dare, na rasa mafari na rasa dalili na rasa meyasa hakan ta kasance dani,
Zan gyaru zan gyaru nayi maka aik'awari Dadyna.... ABDUL yakai qarshen zancensa da zubda hawaye.
Ai nan take qaunarsa taqara cafkar zuciyar Dadyn, nan ya rungumesa yana cewa. "Nagode my son Allah yayi muku alkarka dena hawaye,  nasan zaka dawo yanda kake da, yanxu kira AMEER ka dakatar dashi zuwa gidan Alhajin daka yanka dan yace saiyaje yayimai aika aika.
Zare jikinsa ABDUL yayi batare dayace komai ba yahau kiran number na AMEER' Yana d'auka Yace dashi.. "Dan uwa kashare batun zuwa gidan Alhajin nan pls, dan baqaramin b'arma nayi mai ba.

AMEER dake cikin motarsa bakin wani keb'abb'an shago yana jiran abokansu su fito daga shagwan dan sun shiga siya masu kayan maye ne. Sai kawai yaga kiran wayar ABDUL..
Nan ya d'auka bayan yaji abinda Abdul d'in yace mai sai yayi murmushi dacewa.. "Saifa naje dan yasan suwa ya tsaya yana zagi.
ABDUL yaja numfashi da cewa. "Tunda nace maka kashare ka share mana
"Na share d'an uwa.
"Yauwa to yanxu kana ina.
"Ina wajen shagwan Ali nasa su Abba tab'are su siya mana harka.
"Yayi, yanzu ina kan hanyata tazuwa gida kasameni cikin d'akina..
"Ok babu matsala sai munxo.

Sai ABDUL ya kashe wayar da kallan Dady yace. "Komai ya wucce Dady, bashi ba zuwa gidan, ka kwantar da hankalinka, "toh naji dad'i my son Allah yayi muku albarka, "ameen  ABDUL yace sai Dadyn yaja motar suka bar kan haryar.

Akofar gidan nasu Dadyn ya saukesa, Nanko ya shiga cikin gidan nasu dajin wani nishaɗi, irin yanxu akazo aka fitar dashi daga gidan yanxu kuma aka dawo dashi.

Direct d'akin Hajjiya Kakah yayi, nanko yaganta ita da ZAINAB sunyi jugum amma suna ganinsa nan suka saki fara'a ZAINAB tatashi da sauri takama hannunsa.... Saidai nan take tayi saurin sake hannun nasa, shima cikin tsoro yajanye hannun nasa harda b'oyesa a bayansa.
ZAINAB tace "Jikinka  shocking yakeyi ABDUL.
Murmushi yayi da cewa.  "aa Aunty nakine yake shocking d'in, dan daga jikinki ya fito.
Nan ZAINAB tahau kallan jikinta atsorace tana dube dube da cewa "dan Allah da gaske kakeyi, pls karka tsoratar dani.
Murmushi ya qarayi da faɗin. "Toh jeki tab'a Hajjiya Kakah mugani.
Nan tatab'a Hajjiya Kakah amma bataji komai ba, hakan ne yasata sakin ajiyar zuciya ta hararesa da cewa, "kasan Allah na d'auka da gaske kakeyi,
Murmushi dai ya qara sakar mata da basu labarin Dadyn AMEER ne ya fito dashi, Nanko suka dad'a yimai nasiha ya nuna yajisu dayin shashinsa' mama Saude ta sauke labulan windanta zuciyarta cike da dakaicin yanda ana kamasa yake fitowa, kwafa ta iya yi kawai dan ba yanda zatayi..

Shiko ABDUL bayan ya shiga d'akin nasa fad'awa kan katifarsa yayi Wanda take yashe a qasa kan kafet, d'akin natsaf dashi irin na mazaje masu tsafta. Ba komai a d'akin daga katifar sai kayan kallo sai durowa sai tarin littattafan addini dana turawa komai dai a kintse tsaf gwanin ban sha'awa. Kafet d'innan tas dashi sai tashin kamshin d'aki yake..
Nan yaja wayarsa ya bud'e data dan yaga wata wainar ake toyawa a yanar gizo, saidai bai kaiga nisa a dube duben nasa ba' wani wan mahaifinsa me suna Baba Shehu mafad'ici, suna kiransa da Baba. Nan ya banko ƙofar ABDUL d'in afusace kamar zai tashi sama yahau ce dashi... "Kai dai kam kai dai kam anyi yaran banza yaran hofi mara mutunci wanda baisan mutuncin mutane ba, yanxu ba wanda ya isa ya gaya maka kenan kaji, lokaci d'aya ka maida kanka d'an iska d'an bura'uba me shaye shaye tantiri, angaya ma yanxu rayuwar dakasa agaba rayuwace me kyau, kabi ka raina kowa baka ganin kowa da gashi dan tsabar tantirancewa, to wallahi bari kaji' nagaji dajin magana akanka atareni kan hanya ana gayamin, duk randa kaqara aikata wani abu Wallahi saika bar gidan nan dan ba gidan ubanka bane gidan ubanmu ne, cewa yayi kowa ya yanka ya gida babamu yayi ba bare kace gidan ubanka ne. Idan ka gagari kowa ni bazaka gagareni ba.  Yana faɗin hakan ya juya ya tafi afusacen yana meci gaba da surutan takaici.

Cije bakinsa ABDUL yayi cikin b'acin rai yake cewa a bayyane.. "Ammafa mutumin nan ya raina ni, ya dace na gyara tunaninsa dan yasan dawa yake, yasan ABDUL d'in daya sani da bashi bane yanzu.. Yana zuwa nan a zancensa yayi shuru yana tunanin wane hukunci ya dace yayi masa dan yasan TANTIRANCINSA ba irin na yara qanana bane.🤔..

By AUNTYN LUV💋

HALIN WASU MUTANAN Where stories live. Discover now