Page 2

1.7K 112 0
                                    

'☆´-'☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾'☆•
❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠  
☆ *TANTIRANCI KO KARUWANCI*☆
*.¸¸.*♠ *.¸¸*❆ ¸¸.*🤱🏻¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆
'☆´-'☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾'☆•
{Fad'i alkairi ko kayi shuru)🤫
      A true life story
*Follow me on Wattpad @rahamanalele*

Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆

https://www.facebook.com/groups/354329565057948/
” بسم الله الرحمن الرحيم
Page 2

Sam Salisu bai qare ZAINAB da komai na rayuwa ba.
Komai yanayi mata na rayuwa hakan ne yake sawa kaganta fes kamar wata y'ar tsana. Fatarta  kullum agoge take. Tana dai jin dad'in rayuwa na kayan more rayuwa..
  Matsalarta biyuce arayuwa. Na farko shine bin matan da mijin nata yakeyi da shaye shayen daya keyi. Na biyu shine rashin haihuwanta. Dan yanxu haka watanta tara da auren nasu amma uwar mijinta dake bata santa haka tabi tasata agaba wai bata haihuwa dan maseefa kamar shekara taran tayi ba wata tara ba..😊

___Wannan shine labarin ABDUL D'AN KASADA  da mahaifiyarsa Mama Saude da AUNTYNSA ZAINAB da kakarsa Hajjiya Kakah.

*****************************
Andawo labari..

ABDUL na gama waige wai gensa ya fad'a gidan AUNTYN tasa ZAINAB kasancewar anan bayan layin nasu gidan nata yake sam gidanta baiyi nisa da gidan nasu ba..

Da sauri ya fad'a falan nata da sallama sam bata jishi ba. Sai hakan ya bashi damar b'oyewa cikin wani lungu anan cikin falan nata...
   Gam gagam.. Zainab taji ana buga mata ƙofar falan nata kamar za'a b'alla.. Da mamaki tafito daga kitchen d'inta tana me yarfe hannu da qarema y'an sandan biyu  kallo daga sama har qasa tace.. "Lafiya. meya faru..
Afusace d'aya daga cikinsu yace..."ABDUL D'AN KASADA mukazo nema.. "ABDUL.. Ta maimaita da mamaki. Kana taciga da cewa. Toh baizo nan ba.
"Kinga malama karki raina mana hankali. Dama ance kece kike b'oyesa anan gidan. To bari kiji idan kullum kin saba b'oyesa yau baki isa b'oyesa ba dan lefinsa me girma ne..
Wallahi sai mun shiga ko'ina lungu da sak'o nacikin gidan nan mun zak'ulo shi d'an iska Yaro kawai..

   Dama na gaya muku arayuwar Zainab bata da abin so kamar ABDUL. Kuma duk yanda kuke da ita idan zakaci mutuncin ABDUL nan zata sab'a maka. Sun shaqu iya shaquwa ita dashi. Kowa yasan da wannan shaquwar dake tsakaninsu..
  Dan haka nan take taji ranta ya b'aci da titsiyan da suka sakata agaba suna masu yi mata.. Dan haka cikin tab'e baki tace.. "Rainin hankali kuma na nawa. Ainad'e da raina muku hankali. Tunda nace muku baizo ba aisaiku ba wandanku iska ku qara gaba.
Wane ma rainin hankali ne wannan zaku shigomin gida ina matar Aure kanku tsaye batare da sallama na baku izini ba. Haka dukar takoya muku. To Wallahi baku isa ku shiga ko'ina acikin gidana kucajemin shi ba.
Tunda wanda kuke nema nagaya muku baizo nan d'in ba.
Baku da hurumin daza ku shigarmin gida ina matar Aure mijina baya nan kuhau cajemin shi haka siddan ba..
Dan haka saiku qara gaba tunkan na kulla muku wani sharrin dazaku rasa aikinku dan kunsan ba wanda yakai mace iya sharri. Bare ni kuma da nake matar aure wacce kuka fad'oma cikin gida kamar wasu dabbobi. Taqarashe zancan nata da turo d'an kwalinta gaba alamar duk rashin mutuncin da suke tafe dashi nata yafi nasu.. Dan tasha zuwa wajen y'an sanda ana artabu da ita akan ABDUL d'in.. Sam ZAINAB bata tsoran y'an sanda.

Da matuqar b'acin rai sukace mata haka tace.. Tace haka tace!!!
Rai b'ace suka ficce daga gidan suna masu cewa wallahi saidai in kwana zaiyi agidan amma indai zai fito suna nan suna jiransa akofar gidan nata..
Jan tsaki tayi da cewa.. "Aikin banza.. Tana fad'in hakan ta koma falanta da zama kan kujera mecin mutum biyu tana meci gaba da cewa.. Wato shi ABDUL bazai dena jawoma kansa magana ba ko. Wai har sai yaushe zai dena abubuwan nan ne..
Kai amma mama Saude tacuci rayuwarsa. D'aga hannunta sama tayi🤲🏻 daci gaba da cewa.
Ina rokwanka ALLAH dakayi gaggawar warware Wannan kullin. Kaifa kace muroqeka zaka biya mana buqatunmu. Gashi dare da rana aikina kenan wajan rokwanka kan way'annan al'amuran😭..

HALIN WASU MUTANAN Where stories live. Discover now