71%72&73&74&75

1.4K 70 0
                                    

mmnhanif: RANA DUBU....71

©NWA
   ©MAMANHANIF

EDITOR: UMMUL FADILA

***Cikin d'aga kafada yace" shidai yasani Allah ya kaimu ranar da za a shiga kotun" hmm kanada lauya a hannu ne? "Eh inada lauya zan futa an jima zan masa waya muhad'u a gida inagama kinsan Mustafa ko? "En nasanshi kwarai mustafa yasan aikin sa, nifa ganinake shirme muktar yayi haka kawai ya kagi magana don yabatawa mutane lokaci yabatawa kansa? "Barshi inshi wawa ne ai sharia ba wasa bace kinsan yaran masu kudunnan basufiya yarda da kaddara ba, dabai rabu dake ba wannan rabon ayi yaya dashi? Kinga zokiyi Abinda zai fishsheki" Cikin yanayi na kosawa tace" Allah nagaji Baban ummu" cikin salon datai magana shima yayi" kai Daso keda bakida k'iwa? Zokiji wata magana" a gefen sa ta zauna tareda fad'in" kafiya rigima Baban ummu yanzu fa nazama sai a slow" ayya sannu Daso na baby ya canjamin ke matso kiji Abu d'aya zanyi" hmm ta sauke numfashi" Baban ummu akwai aiki a gabanmu lamarin muktar yana neman tsayamin arai" karki damu kanki koma mene zai faru nidai da Allah na dogara nasan muktar yanada karfin dukiyar dazata bashi damar futu na futo akanki kinsan giyar kudi babu   Abinda bata sanyawa, nikuma da Allah na dogara da kuma ke"

Hannunta tasanya cikin nasa kana tace" kome muktar ya mallaka bai isa ya canja Abinda Allah ya hukunto akanmu ba, nidai nasan ya furta kalmar saki da bakin sa sannan ya rubuta a rubuce kuma duk kotin dazaije a duniyar nan babu wacce zata goyi da bayansa sabida saki uku ya rubuta min, koma dai menene shiyasani Allah yana tare damu nima ina tare dakai domin Ina sonka"

Cikin matsanancin farin ciki ya rungumota a yayin da take bayyana masa sirrin zuciyar ta sai yaji tamkar yaune suka soma son junan su don yaune rana ta farko data futa masa irin wannan kalaman Wanda yajima yana fatan samu saga gareta, cikin wannan yanayi suka faranta ran junansu 'yar damuwar data darsu a ranta take ya wanketa ya maye gurbinta da farin ciki ya mantar da ita wani muktar.

Saida aka idar da sallar isha yasamu damar futa, Cikin saa kuma dayaje gidan saiya tarda Almustafa a gidan duk dai akan maganar ne har sunyi magana da Abba sai karin bayani daya nema a gurin Adamu, Almustafa kwararen lauyane wanda Dane agurin Aminin Abbansu yanada mutuk'ar saa cikin aikin sa tareda tsoron Allah da tsantseni, washe gari ranar har gida yaje don Samsun Karin bayani agurin ta.

Cikin wannan satin haka sukai ta kai kawo wajen ganin sun samu kwakwaran shaida akan saki ukun daya rubuta mata, kasancewar Ammi ta kone takardar dole su samu shaidu don ita kadaice kwakwarar shaidar su saikuma Wanda akayi a gaban su.

,
[8:05PM, 1/21/2017] mmnhanif: Acan bangaren Muktar shima ya tattato hujjojin sa wanda suke kara masa karfin gwuiwar zai samu nasara, cikin satin kuwa? Tunda ya gano gidan Muktar hankalin sa yakasa kwanciya Sam baida nutsuwa kishi duk yabi yarikita Lissafin sa ko yaushe cikin zancen zuci yake yana hasaso rayuwar da Maryam keyi da wanin sa, yanda ya dami kansa haka suma yadamesu a kullum saiyaje gidan ko gajiya bayayi shidai burin sa koda sau d'aya ne yayi tozali da ita, hakan da Adamu ya fahimtane yasashi kafawa ya tsare ya toshe duk wata hanya da zata sanya ya ganta, wannan kuma yayi matukar karawa muktar tsanar Adamu jiyake ksmar ya shakeshi ya mutu yahuta.

Yauma a kofar gidan yayi fakin kana yafuto yaiwa mai gadinsu magana kasancewar yaga yana yawan zuwa a kwanakin nan yasa yabarshi yashiga harda bashi gurin zama kana yadau waya yakira Adamu ya sanar dashi bakon sa yazo,

Tunkan yayi dogon bayani yasan muktar ne don haka yace yana zuwa, a lokacin dayayo wayar suna falo suna hira tamkar babu kalubale a gaban su don haka yana sane yakama sunbatar matar sa don yasan zata maida martani, aikwa yayi sa'a da kwalliya akan fuskar ta bakin nan yasha man leb'e da jan baki, kan yafuto saida ya tsaya ya kalli fuskar sa a gilas din taga aikwa yaga yanda yakeso yayi murmushin keta yayi gaba.

RANA DUBUWhere stories live. Discover now