43

5.8K 261 204
                                    

_*RASHIN SANI.......*_


*HAUWA A USMAN*
        _JIDDARH_

'''Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh'''

4⃣3⃣

Ido ta zaro cikin tsantsar farin ciki dan tasan matuk'ar suka zo shirin Khulud ya lalace,
tace " da gaske dan Allah Hub..!?

"Uhmmm wannan duk d'okin auren ne..!?

" Hmm bazaka gane bane,
" a'a zan gane idan an fad'a min,
Sanah tayi murmushi had'i da cewa " Hub seriously sun taho..!?

" A'a da wasa nake miki Hilwa bai nan sunyi tafiya da president sai bayan 3 weeks zasu dawo,
idan sun dawo zasu zo,
wata irin razananniyar fad'uwa gaban Sanah yayi tamkar an buga mata dalma haka taji,
cikin ranta tace " انا لله وانا اليه راجعون اللهم اجرني في مصيبتي واكلني خير منها,
ya Rabbi ka fitar da dani daga cikin tsaka mai wuya ka zab'a min abinda yake alkhairi a gare ni,
" K'ALB ya kika yi shiru..!?

Yak'e tayi wanda yafi kuka ciwo tace " ka rik'e a ranka ina matuk'ar sanka sosai,
ba kuma zan tab'a yin abinda zai cutar da kai da rayuwarka ina sane ba,
" I knew yace yana dariya,
"My life yanaji ki kamar a waje..!?

" Eh na raka my Khulud unguwa ne,
" ok take your time idan kun koma gida ki kira ni,
" ok badamuwa I love you so much,
" I love you too,
murmushi kawai Khulud tayi batare datace komai ba,
bayan sun koma gida sunci abinci,
Khulud tace " bari nayi wanka sai mu fita muyiwa Abbu maganar bautar k'asar..!
Sanah batayi magana ba, tayi shiru,
Khulud ta shiga wankan, safa da marwa Sanah ta soma yi tana tunanin mafita da abinyi,
tana cikin haka Khulud ta fito,
duk da ta lura da halin da Sanah take ciki,
amma sai tayi burus tamkar bata lura ba,
kayan Sanah ta saka kasancewar bata zo da kaya ba,
kallo d'aya zakayi mata ka fuskanci tana cikin tsantsar farin ciki da annashuwa,
batayi mata magana ba, ta rik'e hannunta sukayi parlor dan taji muryar Abbu,
zama sukayi kusa da dashi suna hira sosai,
yana kuma basu lokacinshi sosai,
kallan Sanah Khulud tayi, tayi mata alamar tayi mishi maganar,
amma Sanah tayi burus tamkar bata san abinda Khulud ke nufi ba,
k'afa Khulud tasa ta tab'o Sanah had'i da motsa lips d'inta tace " talk..!,
ta fad'a yadda babu mai jinta,
still shiru Sanah tayi, ganin bata da niyyar yi mishi magana yasa Khulud,
cewa " hmmm Sanah ba tare kuka fara BUK dasu Wajnah ba ne..!?

"Eh..!, tace
batare data kalle ta ba,
" naga suna maganar tafiya service next week,
ya banji ke kina maganar ba..!?

" Eh..! so nake sai takardar ta fito sannan sai na fad'awa Abbu,
kallanta Abbu yayi kai badai har bautar k'asar tazo ba..!?

Karaf Khulud tayi tace " wallahi kau Abbu ai abun ba wuya,
gashi nima har nayi 3yrs da aure,
kuma tun kafin inyi aure ta soma fa,
" kai masha Allah, yanzu shekara ta zama kamar kwana,
babu wuya kaji ta zagayo,
" eh nima dana ji su Zohal na maganar nayi mamaki,
dan k'in yarda Papu yayi sai da yaje har makarantar ya tambaya,
murmushi Abbu yayi yace " ai ba'a k'arya da bautar k'asa,
kuma duk inda mutum yakai da wayo da lura akan yaran yanzu sai dai idan basu ga damar yin abun ba,
sai dai kawai mutum yayi iya k'ok'arin shi ya barwa Allah sauran,
ka kuma yi addu'a, ka tsarkake zuciyarka akansu,
shine kawai mafita,
ajiyar zuciya Khulud ta sauke cikin tsantsar farin ciki,
tace " that's why I really love you my Abbu,
kuma kasan our Sanah she will never hurt, chet and betray us,
murmushi yayi yace " haka ne kam Allah ya taimaka,
suka amsa da Amin,
ita dai Sanah shiru tayi har suka gama hirarsu,
suna komawa bedroom Khulud ta kira Papu ta sanar dashi yadda sukayi da Abbu,
yace " good in sha gobe zan kawo miki foam d'in,
ta amsa da to had'i da yi mishi godiya,
duk yadda Hanash yaso Khulud ta koma gida k'in komawa tayi,
dan gani take muddin tayi sake tabar gidan komai lalacewa zayyi,
akan dole ya hak'ura ya barta.

RASHIN SANI......!!! Where stories live. Discover now