Chapter 24

683 67 9
                                    

💞 JINAH (Matar Aljani)💞
by Malik al-Ashtar ✒️

On wattpad 👉 https://my.w.tt/g6epSX3tJ5

You'd like this New ❤️ Story

CHAPTER 24

~*Wilaya Writers association of Nigeria*~
(Home of peace & hospitality).💦we are here to educate and entertain the heart of readers,we are the best among the rest💦

Visit to like our page:https://www.facebook.com/Al-wilaya-writers-association-of-Nigeria-113198586763490/?referrer=whatsappwhatsapp

Ana yawan fadar cewa duk ana haihuwar mu ne a matsayin mutanen kirki, idan kuma daga baya muka zama miyagu, dalilin irin tarbiyar da muka samu ne, da irin jarabawowin da muka gani da kuma dalilin mutanen da ke kewaye damu... Wata kila haka ne, domin muna zuwa duniyar nan ne bamu san komai ba, bamu iya komai ba, komai muna koyonshi ne anan. Ta dalilin wasu da muke ganin suna aikata abun.

Nasan kun taba ganin yaro na kwarai da zuciya mai kyau amma kuma gidan da ya fito, tasu zuciyar ba mai kyau ba ce? Akwai kuma wani yaron wanda bakar zuciya gareshi, amma gidan su mutanen kirki ne.

Haka akwai wani wanda cikin rayuwarshi, ya taso a na kwarai, rana daya zai juye zuwa mugu dalilin wani abu da aka yi masa, ko kuma wata rayuwa da yake fuskanta...

Toh Fally yana cikin irin wannan rukunin na masu sauya halinsu, kamar an tsoma zuciyarshi cikin ruwan kwalta ta tashi daga launin ja zuwa bakakirin har taso tafi kwaltar baki. Kiyayya ta rufe masa ido, shi da ba zai iya cutar da wani ba ma, amma yau gashi yana cutar da abar kaunarshi wadda a shirye yake ya sadaukar da rayuwarsa saboda ita. Kamar yanda yake yi a halin yanzu. Tana son ta bude ido, amma ya sanyata cikin doguwar suma.

-Baba, me yasa mama taki tashi?
Ayu ya tambayi baban nashi.

-Saboda tayi sadaukarwa saboda ku, saboda ita ne muke har yanzu a raye.

-Kamar yaya, me ta aikata?
Aya ta tambaya.

-Toh zata farka?
Shima Ayu ya kara jefo wata tambayar.

-Eh, amma kuma dole sai na kaita wani guri mai nisa, nesa da nan.

-Toh me muke jira, mu tafi mana!

-Hakan ba sauki gareshi ba, ku ba zaku bimu ba.

-Toh me yasa haka?

-Inda zamu je, basu son da akwai ku ba, kuma idan kuka bimu, zasu ce ku zaku zama fansar ceto mahaifiyar ku. Kuma kunsan mamarku ba zata taba yarda da hakan ba, nima kuma haka. Nasan Sarah zata kula da ku har lokacin da zamu dawo.

Karyar da Fally ya shiryawa yan biyu kenan ba tare da sun harbo jirginshi ba. Yasan idan yace masu zai dauki Jinah ya tafi da ita, ba zasu yarda ba har sai ya fada masu dalili. Yanzu kuwa ya riga da ya karance su, idan zai fada masu wani abu, kuma yasan karya ne, to sai ya fara fadar wani abun da yake gaskiya. Gashi kuma ya hanasu binciken tunanin mutane.

-Ya kamata naje yanzu, domin duk wata dakika barazana ce ga rayuwar ta, zan shiga jikinta domin fadawa yan gidan zata je wani guri.

-Baba kana da tabbacin wannan ita ce mafita?
Ayu ya tambayeshi cikin rashin yarda.

-Domin mahaifiyarku zan yi wannan, domin na ceto ta.
Ya bashi amsa.

Shiga jikin Jinah yayi tare da fitowa daga cikin dakin. Tarar da Sarah da su Nafi tayi waje sannan tace masu :

-Zan fita, yanzu na dawo.

-Ina zaki je ne Jinah?

-Ba dadewa ba zanyi.

 JINAH (Matar Aljani)Where stories live. Discover now