Chapter nineteen

382 29 8
                                    

✨ *MATANA* ✨

*Mallakar*
      AUTAR MAMA

*FREE BOOK*

*EXQUISITE WRITER'S FORUM*

*Comment*
*Vote* &
*Share* Fisabilillah

*My WhatsApp group link, Dan Allah mata kawai*
https://chat.whatsapp.com/BrUNywiBsPxDJjxclwHfdU

*019*

           "Aysha! Ya faɗa yana kallonta tun daga sama har ƙasa. "Gwapo! It's You! Ta faɗa da karfi tana karasowa inda yake farinciki fal fuskarta.. "Shekaru dayawa! Ka canza sosai, you look more attractive and handsome, anyway ya bayan rabuwa? Yasu Abbas? Da sauran class mates? "Abbas ya koma Sudan, sauran class mates kuma wasu ba'a ƙara haɗuwa ba, so tell me about yourself" Murmushi tayi tana fad'in " Nothing interesting! I'm here with my dad and you? "Kina nufin bakiyi aure ba? "No, nayi but an raba auren! It's a long story though! Buddy ka ga yadda ka ƙara zama babba? Ta faɗa tana dariya. "Kema haka ai, kin girma kamar ba childish Aysha ba, atom din ajinmu wadda ta fi kowa rashin ji" Dariya ta kuma fashewa dashi tana kallonsa ta ce, " Yanzu dai nafi karfin ace min Atom, na girma, kaifa faɗa min kayi aure? And what are you doing here? Shafa kansa yayi kaɗan kafin yayi magana ta sake cewa " Oh sorry, naga kamar yanzu ka dawo kuma na tsayar da kai and you look so tired! I have noticed that gwapo, don't mind me, mu shiga ciki" "Are You sure? Ya faɗa yana dariya. Itama dariyar tayi tana karbar katin hannunsa ta buɗe sannan ta shiga. Shima shigowa yayi yana kallonta, haryanzu be daina mamakin ganinta ba. "Zauna, bari na kawo miki abin tabawa" "No no no no, kar ka wani damu, kaje kayi uzurinka let me watch movie" Daga haka ta kunna kallo. Murmushi yayi yana wucewa daki, haryanzu halinta na nan she's free minded! Bai dau lokaci ba ya fito cikin casual wears.. zama yayi a kujerar yana fad'in " So faɗa min abubuwan da suka faru bayan munyi graduation na SSCE. Dariya tayi tana cin cookies din data dauko a fridge dinsa ta ce, " Labarina is not interesting na faɗa maka, ka faɗa min naka instead" Gyada kai yayi kafin ya ce, " Ok... Bayan munyi Candy na samu admission kuma kinsan dama marketing nace miki zan karanta, akansa nayi degree da PHD so na fara aiki a chan Nigeria sai na samu offer shine nazo nan, ban daɗe anan ba" "Woow! You are such a lucky man, i said this before right? Ko kamanta? Kai ya girgiza alamar a'a yana murmushi.. "Kana nufin bakayi aure ba all this years? "Nayi! Ya fada a hankali. "What? Is she Dead? Naga duk yanayinka ya canza.. murmushi yayi yana girgiza kai ya ce " tana nan da ranta, tana 9ja" "She's lucky I guess, anyway ni bari nazo na tafi, dama cewa Daddy nayi zan je siyayya kuma na sauka a cab zan shiga store din dake opp dinka na hango kamar kai ashe kai dinne, ga wayana samun digits dinka sai mu dinga gaisa, I'm so happy wallahi" murmushi yayi yana karɓar wayarta ya saka mata numbersa ta ƙasar. "Thanks alot"  Har kofa ya rakota yana murmushi. Yarinyar akwai surutu dama chan. Gyada kai yayi yana komawa ciki. Bedroom ya koma ya kwanta yana lumshe idanunsa.

*9ja*

        Zarah na zaune a front seat din motar Ammar, dawowarsu daga asibiti kenan wajen ganin babyn Bilkisu yaron ya kara girma kasancewar yana samun kulawar ɗaya kamata.. ita sam batayi niyyar zuwa ba amma kasancewar kar Ammar ya ga ko tana kishi da ɗansa ya saka ta bishi.... Kallonta yayi ya ce, "Yau Inna zata ga kin dade, me zaki ce? " Zance na zauna karatu! Ta bashi amsa ba tare da ta kalleshi ba.. "Zarah kalleni" Ya fada idanunsa akanta. Kallosa tayi tana fad'in " Menene? Shuru yayi yana kallonta da kyau kusan minti biyu kafin ya sauke ajiyar zuciya.. "Sauka! Ya fada yana tayar da motarsa. "Menene wai? Cewar Zarah kamar zatayi kuka. "Bakomai, zan tafi ne" ya bata amsa very calmly. "So haka zaka ce min kamar kana korata? Why not in a romantic way" Ta fada tana kokarin buɗe motar. Danna mata lock yayi yana firzar da iska me dumi ya ce, "Did you missed your period? Sai da gabanta yayi wani irin mummunan faduwa har tsoran dataji ya bayyana a idanunta. " Me...meyasa zaka min wannan tambayar? "Just answer me, yes or no? Shuru tayi ta shiga tunani.. tabbas ya kamata ace taga al'adan ta tun satittikan da suka wuce amma kuma gashi har yau, and tana yawan tofar da yawu ga kasala da zazzabin asuba... Da sauri ta kalleshi tana girgiza masa kai hawaye na taruwa a idanunta.. " Kinyi Shuru"  kuka ta saka masa tana girgiza kai.. ajiyar zuciya ya sauke yana kallon ta ya ce " Kema kinsan kina da ciki? Kai ta girgiza kafin ta goge hawayenta ta ce " Bani da wani ciki Allah dagaske.. Shuru Ammar yayi yana jin wani irin baƙin kishi ya tokare masa ƙirji, lokaci daya kirjinsa ya dau zafi.. "Sauka, zan wuce! Ya fada dakyar yana kokarin hadiye halin da yake ciki.. "Ni dai dan Allah ba ciki bane! "Idan ba ciki bane menene Zarah! Bakya ganin kanki? Bakiga yadda kika dawo ba? Your breast are more bigger than B4! Look at your eyes, your skin! Your behavior! I know my profession very well! Just get out! Ya ƙarashe maganar cikin tsawa. Kuka ta saki me karfi duk ta tsorata, ga zancen ciki da yace tana dashi ga ihun da yake mata. Dukan stairing motar yayi da ƙarfi yana jin wani irin abu a wuyansa. "Zarah get out please! Ya kuma faɗa gaba daya bacin rai ya bayyana a fuskarsa. Kai ta girgiza masa tana riƙo hannunsa ta ce " Na rantse bani da ciki" "Kin rantse? All this symptoms fa? Zaraaaaaah! Ya fada yana runtsa idanunsa... Babu wanda zai iya fahimtar halin da yake ciki, shi kanshi kasa gane kansa yayi, ji yake da zaiga Mustapha sai ya masa dan iskan duka.. Ni kuwa nace sannu isasshe, aikin banzaa kai😒. "Zanzo gobe zamuje asibiti, stop crying"  Gyada kai tayi tana goge hawayenta. A sanyaye ta sauka tana jan kafafunta.. Tana fatan ace ba ciki bane dan bata san yadda zataji dashi ba.  Bata tadda inna a tsakar gida ba, daki ta wuce ta ganta zaune tana lazimi kafin a atayar da sallar magariba. Kwanciya tayi tana lumshe idanunta... Washe gari da safe ko makaranta bata je ba tace da Inna asbiti zataje.. karfe 9am Ammar yazo. Front seat ta zauna cikin sanyin murya ta ce " Ina kwana? "Lafiya lau" daga haka be ƙara cewa komai ba.  Bayan sun isa asibiti a office dinsa ya zaunar da ita sannan yayi round, kusan 1hr tana zaune sai gashi yazo.. syring ya ɗauka yana kallonta ya ce " Taso muje lap a ɗauki jininki" Gyada kai tayi tana tashi ta bishi.. basu daɗe ba aka dau jinin suka dawo. A kasalance ta ce " Ba gida zan koma ba? "Eh yanzu result din zai fito kwanta a nan" ya faɗa yana nuna mata kujera. Kwanciya tayi tana lumshe idanunta. Ta daɗe tana bacci be tasheta ba. Har kusan 2pm sannan ta tashi. Kallonta yayi na ƴan seconni sannan ya dauke kansa yana fad'in " Ga toilet nan, idan kin fito kiyi sallah" "Har anyi azahar? Banza yayi mata. Itama bata kara cewa komai ba ta tashi ta wuce toilet ɗin daya nuna mata, kafin ta fito har ya shimfida mata sallaya, bayan ta idar da sallah ta nufo inda yake ta ce " Me result din ya ce? "Positive! Kina da ciki har na wata daya da sati uku" Shuru tayi zuciyarta na tsananta bugu. "Why are you shocked? Kinfi kowa sani ai! "Wallahi bansani ba" ta fada tana hawaye.. Tashi yayi yana matsowa daf da ita ya ce " Oh a ruwa kika sha cikin? Runtsa idanunta tayi tana jin nunfashinsa a kan fuskarta. Fuskarta yake bi da kallo daga bisani yayi saurin matsawa daga inda take yana komawa mazauninsa. "Ki kira mijinki ki fada masa" "Ni babu wanda zan fadawa, dan Allah Ammar ka zubar min Wallahi ban shirya haihuwa ba! "Oh really? Baki shirya haihuwa ba amma kin iya kwana da miji right? Toh ba ruwana, kuma billah na ƙara jin maganar zubar da ciki a bakinki ranki sai ya baci! Wuce in kaiki gida! Riƙeshi tayi tana kuka ta ce " Dan Allah Ammar dan soyayyar da mukewa juna ka taimakeni wallahi bana son cikin nan dan Allah" "Zarah! "Na'am! Ta amsa a sanyaye. Hannu ya saka ya share mata hawaye yana kallonta ya ce " Kar na sake ji! Na fada miki! If not billah ranki zai ɓaci" Kuka ta fashe dashi tana hugging dinsa very tight.. runtsa idanunsa yayi yana jin wani iri a zuciyarsa. " Zarahh! Ya kira a hankali. "Ammar bana son haihuwa da Yaya Mustapha, Ammar kai nake so Dan Allah ka cire min cikin nan dan Allah" banbareta yayi daga jikinsa yana kallonta ya ce " Indai kina sona dagaske toh karki zubar da cikin nan, idan kuwa kika zubar nasan matsayina" Fuskarsa take kallo zuciyarta na ƙara melting, sosai take jin masifaffiyar kaunar Ammar din! Amma an cuceta da aka rabata dashi aka aura mata wani! Bata taɓa tunanin zata dinga aikata abinda tasan cewa lefi ne a wajen Allah amma kuma ta take sanin saboda san zuciya ba. "Ina kaunarki Zarah, but Allah knows the best, so ki bar masa komai kinaji ko? Kuma ki raini danki.. sake rungumeshi tayi tana hawaye. "Zaraaah, ya isa mu je gida" Sakinsa tayi tana goge hawayenta zuciyarta na zafi.. (Kuskurene babba kina matar aure ace kuma baki rabu da tsohon saurayinki ba musanman ace irin auren Zarah da Mustapha ne, wato zarah tana da wanda take so aka aura mata Mustapha, shiyasa auren dole bashi da daɗi kuma babu kyau, duk da cewa ita zara'u Ƙin magana tayi tun farko kuma wannan ma kuskure ne! Allah yasa mu dace mufi karfin zuciyarmu Amin) A gaba da gidansu yayi parking din motarsa sannan ya mayar da dubansa gareta, har yanzu hawaye takeyi. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana kiran sunanta. Hawayen fuskarta ta goge ba tare da ta kalleshi ba ta ce, "Nagode! Daga haka ta sauka. Inna na tankade ta shigo sai jan kafa takeyi. "Gaskiya ki kwaso rana, amma kin tadda layi ko? Zarah zatayi magana amma kuka ya kufce mata. Yarda rariyar tankaden Inna tayi tana tasowa ta riketa... "Ke lafiya? menene? Kasa magana tayi saboda irin kukan da takeyi, riƙota Inna tayi suka shiga daki, a gefan gado ta zaunar da ita tana fad'in " Faɗa min mana" "Inna wai ciki ne dani!  Ta faɗa tana kuma rushewa da kuka.. "Ciki? Inna ta fada cikin tsantsar farinciki sai kuma ta riƙo hannunta tana fad'in " Ba kuka zakiyi ba kinji? Godewa Allah zakiyi, mutane nawa ke auren shekara da shekaru sai kiga basu haihu ba? Ke kuma gashi daga yin aure? Goge idanunki kar na kara ganinsu kinaji ko? "Inna makaranta fa? "Ai baki da matsala zara'u, ki godewa Allah bame laulayi bane, kai Alhamdulillah! Inna ta ƙarashe maganar tana daga hannun ta sama. Kafin dare har Inna ta kira Ummi ta sanar da ita, Ummi ta sanar da Daddy, Farida, Zainab da kuma uban gayya Mustapha. Zara'u na kwance tana duba littafinta kiran Mustapha ya shigo kamar bazata dauka ba amma dai ta dauka tana fad'in " Ina yini? " Zan kiraki vd call please yanzu" daga yanayin muryarsa ta gane an sanar dashi da maganar cikin. Katsewa tayi ta hau online aikuwa sai ga kiransa vd call. Dauka tayi tana fad'in " Me zaka gani daka kirani vd call? "Cikina mana! Ya fada baki har kunne. "Uhm" Cewar Xarah tana dan juya idanunta. "Pls cire rigar ingani"  "Babu fa abinda zaka gani cikina yana nan yadda yake" " Ok then yaushe kika je asibiti? Kuma symptoms kika fara ji? "A'a kawai zuwa nayi dan ina zazzaɓi shine da aka min BT sai ya nuna" Murmushi yayi me kyau yana kallon fuskarta ya ce, " Ina kaunarki Zarah! Shuru tayi ba tare da tace komai ba. " Ok wata nawa cikin namu? Ya kuma fada. "ɗaya! Ta bashi amsa a takaice. "Allah ya saukeki lafiya My Zarah, ji nake kamar na buɗe ido na ganni a 9ja, but insha Allah zan dauki permission zanzo, amma Please Zarah let's go back together, please! "Wai karatuna fa? Ni gaskiya ba inda zanje" "zan nema miki wata makarantar anan, kullum fa cikin azumi nake kinsan dai bazai yu nayi tayin azumi ba kinsan kuma ina da ulcer" "Ai lada zaka samu" murmushi yayi kafin ya ce, "Na sani, but shima ai ladan zamu samu har da ke" Batace komai ba kuma ta dauke idanunta daga kallonsa.. " Take care please, banda shan kayan sanyi, ko da yake ma ai ba sai na faɗa miki ba kinfini sani Future Registered Nurse ko? Murmushi tayi tana fad'in "Insha Allah! "Yawwa kun fara zuwa asibiti practical? Kai ta daga alamar eh. "Good Allah ya taimaka, insha Allah idan nazo tare zamu koma ko?  Kai ta girgiza a'a. "Dan Allah mana Zarah! Zaman ba daɗi ni kaɗai i miss You alot duk da cewa ba ji dani kike ba" Taɓe baki tayi tana hamma ta ce, "Bacci zanyi sai da safe" "Ok, i love you" bata amsa ba sai kallonsa data tsaya yi kiss yayi mata blowing.. katse wayar tayi da sauri tana ɗanyi tsaki. Tun daga wannan lokacin Zarah ta ƙara ganin gata wajen mijinta da kuma uwar mijinta amma ita sam ko a jikinta musanman kulawar da Mustapha yake nuna mata yanzun gani take duk takurawa ce, har ya fara siyan kayan baby, tun abun na bata haushi har ya fara bata dariya.....

MATANA ✓Where stories live. Discover now