Jininku ce....

8.3K 339 14
                                    

BISMILLAHIR RAHMANEEN RAHEEM

NAGARTA WRITER'S ASSOCIATION

SANADIN HAD'UWAR MU
©Pharty BB

(1)

ANGUWAR LIMAN
Anguwar liman wani k'auyene dake jahar katsina a kar'kashin k'aramar hukumar Batagarawa.
'Kauyene da Rashin Ilimin Boko da Islamiyya yayi 'karanci, K'auyene da jama'a cikinta suke fama da rashin wadatattcen ruwa balle wutar lantarki, babu hanyar mota sai burji saboda halin ko in kula da gwamnati ta nuna akan garin.
Akasarin mafi yawancin mutanen garin Fulani ne sannan kuma manoma ne, sukan noma hatsi su kai cikin birni su sayar, a haka dai suke rayuwar su.

Yammacin Wata Litinin
Yarinyace y'ar kimamin shekaru goma sha biyu a duniya, sauri take sosai kanta d'auke da tulu sai hard'e kafafuwanta take sakamokon saurin da take yi, Allah-Allah take ta isa bakin rafin ta d'ibo ruwan da mahaifinta ya sata dan a samu a dafawa mahaifiyarta magani dashi, da isarta ta samu layi a bakin rafin kasancewar shine babban rafin garin kuma ruwansa yafi kyau, rokonsu ta fara yi tare da durkusawa ko zasu tausaya mata, duk da sun girmeta a d'ari d'ari take rokonsu karsu mata duka dan tasan halinsu da sun girmi yaro dukansa suke a kauyen.
D'aya da suke tsayene cikin 'yan matan k'auyen ta kalli k'awartan dake zaune kusa da ita ta juyar da kai.
"Ramme kiyi magana mana, kinsan waccan mayyar ba barinmu za tayi ba in bata d'iba ba."
Wacce aka k'ira da Rammen ne ta juyo ta watsawa Ummu dake tsugunne wani kallo, cikin tsawa tace.
"Matsamin daga nan kar naci ubanki shegiya bak'a mummuna."
Cikin sauri ta matsa gefe tana sharan kwalla, sai da suka gama iskancin su da iyayinsu kafin suka d'au tulunsu su kayi gaba, sai lokacin Ummu ta samu ta d'iba ruwan sauri-sauri ta baro wajen, a haka har ta iso gidansu dake kewaye da zana da kaba da d'akin biyu na jar k'asa sai dan kewaye na kiwon kajin Babanta guda biyu sai kewayen band'aki.
Da sallama ta shiga ba kowa tsakar gidan, d'akin mahaifiyarta ta shiga nan ta tarar mahaifinta zaune kusa da mahaifiyarta yana mata firfita saboda zafi ga zafin ciwo, kusa dasu ta k'arasa tace.
"Baffa ga ruwan na debo layi na samu, Inna sannu kinji."
Ta fad'a tana goge hawayen fuskarta, kallonta mahaifinta yayi yana mik'a mata maficin hannunsa.
"Zoki mata firfita bari insa Abu ta d'aura ruwan."
Karban maficin tayi ta fara mata firfita shiko ya fita ya nufi d'ayan d'akin, sallama yayi shuru ba amsa, labulen d'akin ya daga yaga wayam bata nan, komawa yayi ya nufi inda suke ajiye dan kara da budu da suke hura wuta, d'auka yayi yasa a murhunsu da manyan duwatsune guda uku, dakyar ya hura wutan ya d'ora ruwan maganin da aka bashi, bayan ya tafasa ya juye a daro yakai wani d'an karamin bangida an kewayeshi da zana da langa langa, bayan yakai yaje d'akin ya taimakwa Inna ta fito ya kaita bangidan, wanka tayi da ruwan maganin ta fito ta koma d'akin ta kwanta, lokacin ana kiran sallar la'asar, alwala Baffah yayi ya musu sallama zai tafi masallaci.
Bayan tafiyarsa da taimakon Allah dana Ummu Inna ta samu ta fito da guntun ruwan da Baffah yayi alwala tayi dakyar ta koma d'akin, nan itama Ummun tayi yar shafe gudun kar ruwan ya kare kuma ba dama su tab'a na Abulle, zaune ta tarar da mahaifiyartan tana sallah duk da ba yau ta saba ganinta tana sallah haka ba amma duk lokacin data ganta sai taji tausayinta duk da kasancewarta k'aramar yarinya sosai amma tanajin tausayin mahaifiyarta.
Sallah tayi ta fito tsakar gidan ta share ta wanke kwanukan da Abulle da yaranta suka b'ata ta saka itace a murhun kamar yanda Abulle ta koya mata kafin ta koma d'aki, kusa da Inna ta zauna tana mata firfita can tace.
"Inna banyi wanka ba tin jiya da safe."
Kallonta Inna tayi kafin dakyar ta bud'e baki tace.
"Ki bari gobe in kunje debo ruwa da safe sai kiyi sawu uku a maimakon biyun da ki keyi sai kiyi wanka da d'ayan."
"To Innata."
"Budd'ona Tashi ki shirya makarantar Allo."
"Innah inna tafi wazai kula dake."
"Karki damu Baffanku zai dawo yanzu kuma bana bukatan komai yanzu."
Tashi tayi ta d'auki wani ko'dadden hijab nata duk yasha faci ya mutu murus, bayan tasa ta d'auki Allonta tama mahaifiyarta sallama ta fita, a kofar gidan ta had'u da Abulle da yaranta uku, Dije ta girmeta da shekaru biyu sai Laure sa'arta da Ja'afaru dan shekaru uku.
Durkusawa tayi da sauri tana cewa.
"Sannu da zuwa Dadah, kin dawo lafiya."
Ko kallo bata isheta ba tayi wucewarta da yaranta cikin gidan, Laurece ta tsaya tace.
"Ummu jirani in d'auko allona."
"To." Tace mata tana tashi daga tsugunnon da take, baifi minti uku ba ta dawo d'auke da allonta suka fita a gidan.

SANADIN HA'DUWARMUWhere stories live. Discover now