13

2K 142 2
                                    

NAGARTA WRITER'S ASSOCIATION

  SANADIN HA'DUWARMU
    ©Pharty BB

13

  Kwanaki sun juye sun zama satikai, sati ya juye sun zama watanni, watanni sun shud'e sun zama shekaru biyu.
Tin lokacin baya tsakanin Ummu da ahlin gidan Alhaji. Sulaiman Mai Shadda sai dai tsananin bauta da aiki, bata aiki sai aikin y'an matan Mami ba duka ba zagi amma tana bautuwa, tsakaninta da Sadeeq kam sai gaisuwa in ta had'u dashi zata gaishesa ko ba zai amsa ba, bangaren karatu ko tana Jss 3, Masha Allah tana fahimta amma tafi fahimta bangaren Arabic akan boko.

****
  UMARU MUSA 'YAR ADUWA UNIVERSITY KATSINA STATE.
'Yan matane manya da yara, matan aure da budurwaye, tsaye suke filin makarantar y'an bangarori daban-daban (Department) kowanne ka duba fuskarsa murmushin jin dadine kwance suna murnar a yau sun kammala degree nasu ciki harda y'an matan Mami, Biebie da Hauwaty, inda Hauwaty ta karanci Biochemistry, Biebie ta karanta Accounting.
Sun dad'e tsaye filin makarantar suna shagalinsu kafin aka fara watsewa d'aya bayan d'aya.
Bayan sunyi parking motar suka fito da sauri sai Babban falon gidan y'an uwansu har sun fara zuwa dan taya su murnar kammala makaranta ciki harda y'an Funtua da Daura saura y'an Kaduna da zasu zo gobe.
Da gudu Biebie tayi wajen Mami bayan ta rumgumeta ta taya ta murna kafin ta saketa ta fad'a kan Momynta.
"Mommyna."
"Na'am Daughter na, yau dai angama karatu ko."
'Daga kanta tayi tana cewa.
"Mommy saura Masters ."
"Masters ko aure, Masters sai dai a gidanki."
Tashi tayi tabar wajen ciki da kunya ganin iyayenta maza suna wajen, su ko dariya suka saka, suka ci gaba da hiran duniya.

  Washe gari karfe goma y'an Kaduna suka iso Yayan Mami mai suna Alhaji. Saminu da Matarsa Zainab da K'anwarsa dake gabansa bayan rabuwanta da mijinta shekaru shida, sun samu kyakkyawar karb'a kamar yadda aka saba karbarsu, Mami murna ta rasa inda za tasa y'an uwanta da matansu da y'ayansu.
Bangaren Ummu ko baiwar Allah ranar ko makaranta ba taje ba sai dirkar aiki suke ita da Iyamee daga d'aura wannan sai saukewa, girki sunyi yafi kala shida kowa da irin nasa.

  Karfe uku aka fara tafiya wajen babban hall din da suka kama dan bikin kammala makarantarsu, iyaye mata da y'an mata da samari na Ahlin(Family) suka halarci wajen sai y'an makarantarsu k'awayensu, karfe Hudu na yamma aka fara gudanar da bidirin bikin da suka shiryawa yaransu, ansha shagali an wataya anci ansha, y'an mata sun dirka rawa kamar ba gobe, karfe takwas na dare aka watse inda Mami ta bada kyautar motar da Abba ya bawa Hauwaty da Biebie.
Bayan sun dawo gida nan aka baje a babban falon gidan tin daga kan Babban yayansu har k'aramar cikinsu Adda Habiba suna hira abinsu kowa hankalinsa na ga hirin da suke na son had'a auren zumunci, banda kwaya d'aya cikinsu data sa musu ido tana kallonsu.
Nan manya mazan suka yanke shawaran had'a Biebie da Yaya Sadeeq, Samii Yah Mukhtar, sai Hauwaty da Ya Aminu inda za'a d'aura auren nan da wata uku, a garinsu fadar Mahaifinsu sannan ayi biki daga baya akai kowacce gidanta, iyaye mata sunyi na'am da batun dama Hauwaty suna soyayya dashi haka Samii ma da Yah Mukhtar, matsala dai Yah Sadeeq ne kuma shima suna fata ya amince.
"Munira ba kice komai ba."
Fad'in Mommyn Biebie tana dafa cinyar kanwartan.
Murmushin yake tayi dan ita kad'ai tasan me take ji a ranta.
"Ba komai Addah kawai ku manya kuna magana bai kamata musa baki ba."
"Haba ke kuwa ki daina fad'in haka, ki daina ware kanki cikinmu duk d'aya muke hatta Habiba da take 'karamar cikinmu baki ga tana bada nata shawaranba kuma muna karb'a, dan haka ki daina."
"To Addana na daina."
"Yawwa kanwata ko kefa, me zaki bawa yaranki na gudun mowa."
Murmushi tayi.
"Kinsan ni fannin dana fi karfi dan haka biki saura wata zan tattarasu mu tafi in fara aikina kafin ku iso."
"Shikenan kin hutar damu ba sai mun kawo wata ta kalle mana yara ba, Allah kaimu lokacin."
"Ameen." Cewar Munira tana tashi bayan ta musu sallama ta wuce Upstairs, nan ta tarar da y'an matan suna bud'e kyautattukansu da suka samu, samari da y'an mata kawayen arziki da yan uwa duk sun basu gudun mowa banda mutum daya wanda suka fi kusa dashi wato ya Sadeeq danshi ko halartan bikin da suka yi bai yi ba.
Wucesu tayi ta shiga d'akin bata dad'e da shiga ba Biebie ta biyota, da sallama ta shiga bayan ta amsa ta zauna kusa da ita kanta a k'asa.
"Biebie." Adda Munira ta k'ira sunanta.
"Na'am." Ta fad'a cikin muryan kuuka.
"Lafiya, Biebie? Me ya faru?"
Kuka tasa mata harda shessheka, rumgumota jikinta tayi ta hau lallashinta duk da bata san musabbabin kukantan ba, sai da tasha kukanta ta koshi kafin ta fara magana a hankali.
"Anti Munira tsawon shekaru biyar ina sonsa, tin da na taso na mallaki hankalin kaina zuciyata ta kamu da sonsa, Anti duk tsawon lokacinnan bai tab'a d'aga ido ya dubeni da sunan tausayi bama balle soyayya, Anti ya zanyi? Mezan yi ya soni?"
Tana gama fad'an haka tasa wani kukan.
"Hakuri za kiyi Biebie akan wanda ki keyi balle kuma kin kusa zama mallakinsa, ko ba Sadeeq ba?"
Da sauri ta d'ago kanta fuska duk hawaye.
"Anti me kike nufi?"
"Iyayenku sun tsaida ranar aurenku ke da Sadeeq, Hauwaty da Amin, Samii da Mukhtar, nan da wata uku."
Har zuciyarta taji dadi amma kuma tana tsoron yanda Sadeeq zai kar'bi aurenta, a kunyace ta sunkuyar da kanta.
Murmushi Adda Munira tayi.
"Ba kunya tsakanina dake kuma Biebie Love."
Dariya tayi jin sunan data k'irata dashi ta fita da sauri ta fad'a d'akinsu.
Bayan fitarta baya tayi ta jingina da gado a hankali wasu siraran hawaye suka zubo mata tasa hannu ta shere, inda sabo ta saba duk ranar Allah sai ta zubar dasu.

  Washegari har karfe d'aya na rana kafin y'an Funtua, Daura da Kaduna suka d'au hanya, sai y'an matan Samii da Kausar suka zauna dan 'karasa hutunsu a gidan.
Karfe d'aya da rabi ta fito cikin shirinta na Islamiyya dasu ta fara cin 'karo a falo suna zaune, har k'asa ta durkusa ta gaishesu Samii kad'aine ta amsa sai Kausar data juyo ta bita da kallo kafin ta juyo.
"Wannan Babyn fa." Cewar Kausar.
"Y'ar aikice ta samu guri." Rahma ta fad'a tana jan 'karamin tsaki.
"Y'ar aiki dai." Fad'in Kausar na zaro k'ananun idonta.
"Eh Ya Sadeeq ya kawota mana."
Murmushi Kausar tayi a ranta tana k'ara hasko diri na Ummu.
Hiransu su kaci gaba dayi har karfe biyar, Mami ko na wajen mijinta, Ya Sadeeq ko bai dawo ba tin fitarsa na safe.
Karfe biyar da rabi suka taso yanda take dawowa kullum haka yauma ta dawo da shigarta gidan yanda ta tafi ta barsu haka ta dawo ta samesu sai dai Biebie da Rahma basa wajen, jin muryanta yasa Kausar d'agowa da sauri ta bita da kallo harta iso inda suke yanzu ma durk'usawa tayi ta gaishesu da saurinta Kausar ta amsa kafin Samii ta amsa, banda Hauwaty da hankalinta ke kan waya.
Ta tashi zata wuce d'akin ta dan rage kayan jikinta, taji Hauwaty tace.
"Na baki two minutes kiyi kizo ki had'amin cornflakes yunwa nake ji."
"To." tace tana wucewa da sauri ta canza kayanta ta d'aura hijab nata kamar yanda ta saba ta fito ta wuce kitchen shigarta ta d'auki cup ta zuba cornflakes din taga Rahma ta shigo ta tsaya.
"Had'amin black tea."
"To dan Allah bari in ha'dawa Anti Hauwa Cornflakes tana jirana."
"Dallah had'amin ko in make ki stupid."
Da sauri ta ajiye cup din ta fara hada-hadar had'a mata Allah ya taimaketa akwai ruwan zafi, bayan ta gama ta mik'a mata ta fita kafin ta gama had'awa Hauwaty nata ta kai mata.
Kar'ba tayi tana kai bakinta ta dawo dashi ba zato ta watsa mata na cup din jikinta cikin masifa.
"Shegiya kasheni za kiyi, gishiri fa kika samin."
Baya taja a tsorace ita bata lura ba kwata kwata da gishirine tsabar sauri, hannu ta d'aga zata mareta Kausar ta rike hannun.
"Haba Sister budurwa kamar wannan zaki daka, ai ta wuce duka kuma DAN ADAM ajizine yana kuskure, may be garin sauri yasa bata luraba, sorry kinji Sis."
Daga haka ta saki hannunta.
"Da kin barni Kausar na koyawa yarinyar nan hankali dan taga Ya Sadeeq na goyan mata baya zata kawowa mutane iskancin tsiya."
"Sorry Sister a madadinta."
Cewar Kausar na nufan wajen Ummu dake durkushe d'agota tayi ta nufi d'akin ta da ita kan katifarta ta zaunarta.
"Haba Baby bai kamata kina haka ba, kina lura da kyau dan gudun b'ata musu rai, yanzu shiga ki gyara jikinki muje ki bata hakuri."
"To." Ummu tace tana tashi, Kausar na binta da kallo ganin zata shiga Bathroom da hijab ya sata dakatar da ita.
"Baby haka zaki shiga da kaya, d'auki tawul ki rage kayan jikinki mana."
Ita dai Ummu abin natan ko tsoro ya fara bata, wajen kwaba nata tayi ta ciro zani ta nufi Bathroom dashi, gyara jikinta tayi ta fito daga ita sai zani ta rufa dankwalin kayan data cire a jikinta, a tsorace ta fito dan bata saba fita haka ba wani ya ganta, tinda ta fito tasa mata ido zuciyarta na raya mata abubuwa.
Kaya ta ciro ta koma Bathroom tasa kanta fito, murmushi ta sakar mata.
"Muje kiba Hauwaty hakuri."
Ba zato taji Kausar ta damk'o hannunta tasa cikin nata ta damk'e tsam, wani iri taji ta fara kok'arin kwace hannunta ta k'ara rik'ewa gam, bayan isansu ta durkusa har kasa ta ba Hauwaty hakuri, da kyar ta hakura kafin ta tashi ta wuce kitchen dan taya Iyamee girkin dare.
Da dare bayan isha'i wajen karfe tara, zaune take tana duba littafinta na makaranta, taji ana kiranta, ajiyewa tayi ta fita taje wajen gaba daya y'an matan suna zaune.
"Zo nan Baby ni na 'kiraki."
Fad'in Kausar na mik'a mata hannu, kusa da ita taje ta durkusa, kafad'unta ta dafa tayi 'kasa da kanta dai-dai fuskar Ummu.
"Baby had'omin Black tea."
"To." Ummu tace tana tashi dan abin Kausar ya fara damunta, bayan ta had'a mata ta kawo mata gurin karb'ama saida ta rik'o hannunta kafin ta saketa ta wuce d'akinta.
Daren ranar Kausar da kyar ta iya bacci sai juyi take tare da wani kudiri nata daban akan Ummu.

Sadaukarwa ga Ummu Aisha (Ummi Safwaan)

PhartyBb.Wordpress.com

SANADIN HA'DUWARMUWhere stories live. Discover now