6

2.2K 161 2
                                    

NAGARTA WRITER'S ASSOCIATION

  SANADIN HADUWARMU
   ©Pharty BB

( 6 )

  Da asuba da yayi sallah bai koma ba, bayan ya idar da sallah yayi azkhar nasa har gari yayi haske, wanka yayi ya shirya ya sau'ko babbar falon gidan ba kowa dama yasan ba wanda zai tarar dan sai karfe goma ko shad'aya suke fitowa, kitchen ya wuce mai aikinsu tana ta hada-hadar had'a breakfast, tana ganinsa ta durkusa ta gaishesa.
"Ina kwana?"
"Lafiya lau, ina bukatar abinci zan fita dashi."
"To angama bari in had'a."
Bai jira amsarta ba ya fita, cikin sauri ta had'a mishi a warmers masu kyau ta saka basket tak'ai masa parking space, fita yayi direct sai asibiti a hanya ya tsaya a wani plaza kafin ya wuce asibitin.
Bayan yayi parking motarsa ya fito ya nufi female word 'dakin da take ya shiga da sallama tana kwance idonta biyu jin sallama yasa ta kalli kofar ido biyu suka yi dashi ko'karin tashi ta fara yi tana ja baya dan ita tsoro yake bata sosai.
D'auke kansa yayi ya 'Karaso bakin gadon ya ajiye basket da ledan hannunsa bai kalli inda take ba yace.
"Kinyi sallah ko da yake irinku baku damu da bautar Allah ba."
Taji zafin maganarsa amma tayi shuru can ciki tace.
"Banida Hijjab din da zan rufu nayi sallan."
Ledan da ya shigo dashi ya mik'a mata kin karb'a tayi saida ya buga mata tsawa.
"Karb'i dallah banason munafurcin karya."
Hannu na rawa ta karb'a ta diro a saman gadon ta nufi ban'daki, Allah ya taimaketa bangidan da ruwa a bucket a cike, wanka tayi ta dumama hannunta da ruwan zafi ta d'auro alwala ta bu'de ledan, dogon rigane da hijab bak'i, sakawa tayi ta fito kanta a kasa, kwatanta Alkibla tayi tai sallah bayan ta idar ta zauna shuru, shima bangarensa shuru yana zaune a saman kujera duk abinda take yi a idonsa yana kallo ta gefe.
Sun kwashe minti biyar a haka ganin shurun yayi yawa yasa yace mata.
"Ke zoki zuba abinci kici kisha magani in mai daki gidanku."
Hawaye ta fara jin zai mai data gida, gidan data tsana kamar mutuwarta tasan in shi jiya ya ceceta gobe waye zai ceceta.
"Ba kiji mai nace ba." Ya katse mata tunani.
Kuka tasa masa.
"Dan Allah ka mai dani garinmu bana son gidannan."
"Ni a wa, na dauk'owa kaina jaraba KARUWA fa kike."
Sunan daya kirata dashi ya bugita har cikn ranta.
"Wallahi ni ba irinsu bane dole suka min karka mai dani gidannan."
Shuru yayi yace.
"Yanzu yi breakfast."
"Uhmm me kace." Dan tsakaninta da Allah bata san abinda yace ba kauyensu dako makarantar islamiyya babu balle boko.
Ido yasa mata, mai take nufi yanzu ai ko wanda baije makaranta ba in dai a birni yake yasan menene breakfast.
"Ki karya nace."
Sosa kanta tayi ta tashi taja basket din, food flask din tabi da kallo bata san ta inda zata budewa ba sai jujjuyawa take, ganin haka yasa ya sauko yace.
"Bani."
Mik'a masa tayi ya kar'ba ya bu'de ya zuba mata chips ne da ferfeson hanta, tura mata gabanta yayi ya tashi ya koma gurinsa shi haushima ta fara basa yanda take nuna kauyenci zata raina masa hankali.
Da kyar ta iyasa hannu ta fara ci jin da da'di yasa ta faraci ba kakkautawa, sai da taci tayi kat ta tashi ta wanke plate din ta fito lokacin ya tashi daga zaunen da yake.
"Muje ko in maidaki inda na dau'ko ki."
Cak ta tsaya taki motsawa.
"Muje mana."
Girgiza kanta tayi.
"Ka taimakamin ka mai dani garinmu dan Allah."
"Bazan taimakan ba."
"To ka kaini gidan marayu dama Baffana ya rasu Innata kuma ta barni tin ina k'arama."
"Bazan kai kin ba, ke kinga zanfa barki in ki kamin wasa oya muje na kaiki ni zaki rainawa wayo."
"Dan Allah fa nace karka kaini gidannan, zasu b'atamin rayuwa."
"Dama rayuwarki batacciyace, muje."
Zata sake magana ya fizgota ya fara ja tana turjewa, sata cikin mota yayi kafin ya zagaya ya shiga yaja ya fita a asibitin tu'ki kawai yake shi kansa bai san ina yake nufa ba, can wani unguwa inda ba mutane yayi parking, jin ya tsaya ya sata dogo kanta idanuwanta har sun rine tsabar kuka.
"Fita min a mota."
Da sauri ta fara kok'arin fita ya fizgota.
"Dan Allah karka kai ni gidannan."
Buge bakinta yayi cikin bacin rai.
"Yimin shuru dallah, karna kai ki karna kai ki ba nan bane gidanku ko ba anan akaje aka daukoki ba ko zaki cemin duk zamanki gidan Karuwan baki taba iskanci ba."
"Wallahi sati daya da kawoni kuma ban taba yi ba, kuma bada son raina aka kawo ni ba."
Wani kallo ya watsa mata.
"Waya kawoki?"
"Dadah, kishiyar Innata."
"Ina Innarkin?"
"Tana garinsu."
"Ina ne garinsu?
"Ban sani ba."
"Karfa ki rainamin hankali."
"Wallahi na rantse tana garinsu tin ina k'arama ta tafi na dawo daga islamiyya na tarar batanan na tambayi baffana ina take yace ta tafi garinsu."
"Ina Baffanki bai fad'a miki garin su ba."
"Eh, yarasu kuma bai fada min ba."
Jikinsane ya fara sanyi a hankali yace Allah yaji kansa, can ciki tana share hawaye tace.
"Ameen."
Shuru yayi ya 'dora kansa a saman kujera, Taimako shine kalmar da zuciyarsa ya raya masa, kallonta yayi.
"Kinga kar'bi."
Tissue ya mika mata ta karb'a tana share hawayenta.
Numfashi ya sauke yace.
"Kina ji, dole zan mai daki gidannan amma kar kiji tsoro zan bawa wacce take rike daku kudin kwana biyu karta barki ki fita ko wani yazo 'daukarki kwana, insha Allah nan da kwana biyun zanzo in kai ki garinku na miki Alkawari"
Kallonsa tayi ya 'daga mata kai tare da 'dauke kansa.
"Alkawari kayane 'daukarsa da sauki saukesa da wuya, Allah baka ikon cikawa in kuma wayo ko dabara kamin Allah yakawo wani da zai fitarni a cikin wannan halin."
Har zuciyarsa yaji maganarta, motarsa ya tada ta fa'da masa sunan unguwar ya nufa tana nuna masa layin har kofar gida, tabbas dole ko wace ya mace mai daraja da mutunci zata kyamace gidan, shikan sa kyankyamine ya kamasa, kallonta yayi.
"Yimin magana da Hajiyar."
D'aga kanta tayi tana fita, cikin gidan ta nufa da sallama ta shiga kowa na harkan gabansa, babban falon gidan tayi wajen Magajiya, d'urkusawa tayi har 'kasa ta gaisheta, amma tsayawa tayi tana binta da kallon tuhuma ganin suturan dake jikinta.
"Hajiya ana miki magana a waje."
"Wayene?" Ta tambayeta cikin ya mutsa fuska.
"Wani ne za kuyi magana."
"Da mota ko da kafa?"
"Da motane Hajiya."
"Je kice ina zuwa."
Fita tayi taje ta sanar mishi tana zuwa fitowa yayi a motar ya tsaya karkashin wani bishiya dake kusa da gidan irata kan wani dutse ta zauna, fitowar Magayiya shiya katse masa tunaninsa da yake yi, 'karasowa tayi gurin tana binsa da kallo ganin saurayi kyakkyawa d'an kwalisa.
"Sannu d'an samari."
"Yawwa sannu Hajiya."
"Mu shiga daga ciki."
"Ah a Hajiya nan ma yayi maganar ba wani mai tsayi bane."
"Ok ina jinka."
"Dama Hajiya kan yarinyar nan ne, na gani ina so."
Cikin sauri Magajiya ta tare sa.
"Wani irin so kuma, dama kune masu nuna musu so su bijere mana ko, to kaga hanya tin ina ganin darajarkar bar nan gurin kafin in tara maka jama'a."
"Ah a Hajiya baki fahimta bane, so bafa so na aure ba, kudi za ina baki ina d'aukarta muna wuni in ta kama zamu kwana, so bana son yin sharing nata da wani kuma zanyi tafiya nan da kwana biyu shine zan baki kudin kwana biyun karta fita kar kowa yazo ya 'dauketa kafin na dawo."
"Waya fad'a maka ana haka?"
"Alfarma nake nema."
Ya fad'a yana zaro bandir din y'an dubu dubu har gudu biyar dubu hamsin ya mika mata, ganin nairori ya sata muzurai, hannu tasa zata karb'a ya janye.
"Kimin alkawari ba zaki bari wani yayi mu'amala da ita ba."
"Nayi dama ni ita ban takura mata ba ko Badd'o."
Ita kam tinda suka fara maganar ta sunkuyar da kanta sai yanzu jin ta k'ira sunanta ta 'dago kanta.
"Eh ba kyayi."
Ta fad'a ciki ciki.
"Good for you."
Yace yana mik'a mata, ta karb'a tana cewa.
"Sai ka dawo bari in shiga ciki Bodd'o sai kinzo."
Fit ta shige cikin gida, murmushin takaici yayi ya juyar da kansa kanta.
"Ki shiga ciki sai nazo ko, ga wannan ko zaki bukaci wani abu."
Girgiza kanta tayi.
"Taimakon da kake niyar yimin kadai ma ya isheni nagode."
"Karbi nace ba kyauta na baki ba ajiya amma in kinada bukata ki kashe duk ranar da kika samu ki biyani."
Karb'a tayi shi kuma ya nufi wajen motarsa bayan ya shiga ya kallota hannu ta 'daga masa shima ya 'daga mata tare da yin murmushi sai yanzu ta kula kyakkyawane karshe irin wanda suke gani a takarda(mujalla) gashi fari tas.
Suna d'agawa juna hannun har ya bace da ganinta, dakyar taja kafarta ta shiga ciki d'aki direct ta wuce nan ta tarar dasu y'an matan Zulfa bata nan, kwanciya tayi bayan ta boye kudin daya bata ta fad'a tunanin rayuwarta, tin bayan rasuwan Baffanta ta rasa komai nata da duk wani farin ciki da jin dad'in rayuwarta, To wacce tayi SANADIN zuwanta duniyama tayi nesa da ita balle wasu.
Juyi tayi ta gyara kwanciyarta tana k'ara tunanin ko wayo ya mata ko zai taimaka mata, Oho?

Sadaukarwa ga Ummu A'isha(Ummi Safwaan)

 

PhartyBb.WordPress.com

SANADIN HA'DUWARMUWhere stories live. Discover now