18

2K 132 1
                                    

NAGARTA WRITER'S ASSOCIATION

SANADIN HA'DUWARMU
©Pharty BB

18

Da asuba ya rigata farkawa, yayi mamakin ganinta daf da jikinsa kamar zata shige, tashi yayi ya fita ya d'auro alwala ya tasheta kan ya wuce masallaci dake layin unguwar, a tsorace ta farka ganinta saman katifa ya sata dirowa daga saman da sauri ta lalubi hijab tana ta saka ta fita, alwala ta d'auro tazo ta tada sallah bayan ta idar tayi lazimi nata da addu'o'int ta kwanta nan saman abin sallar, tsorone ya kamata duk da tasan Sadeeq ba zai cutarta ba amma tana tsoro kasantuwarsu guri d'aya saboda an fad'a musu a makaranta in mace da namiji sun kasance waje d'aya to cikotan na ukun shaitanne.
Haka ya dawo ya sameta, zama yayi yana lazimi har gari yai haske sosai kafin ya d'an rinsa, karfe bakwai da mintuna ta farka, lallab'awa tayi ta fita, rishion da ta gani ta bud'e taga an had'a an zuba kalanzir da komai, kunnawa tayi ta d'auka kayan miya da duk abinda take bukata ta musu jolof na Macaroni da kifin gwangwani dan ba laifi zama da Iyamee ta koyi girki da dama, bayan ta gama ta bud'e foodflask din da taga gani a kwali alama duk a jiyan ya soyosu dan komai kamar sabone, bayan ta zuba takai d'akin ta wanke plate da spoon ta kai tana shirin shiga dai-dai ya farka daga dan kwanciyar da yake, bayan ta ajiye ya fita wanka yayi ya shigo ta bar masa d'akin ya shirya cikin wani farin yadi me shegen kyau, wani haske ya k'ara da kwarjini.
Bayan ya gama shirin ya k'irata, ita kanta sai da taga ya k'ara mata kwarjini da kyau da kamala, umartanta yayi ta zuba masa abinda ta girki, yaci kad'an kafin ya mata sallama tare da gargad'in karta fita ko ina.
Bayan fitarsa ta samu ta gyara d'akin tayi wanka tayi breakfast ta wanke kwanakun da su 'baci da d'an abubuwan data 'bata, kafin ta kwanta tana ta tune tune nata kalar Rayuwar kenan.

Can Fadar Mai martaba, dumbin mutanen da suka taro tare da shaidu su suka shaida d'aurin auren Sadeeq da Biebie, Mukhtar da Sami, Amin da Hauwaty, Na'im da Kausar, anyi taro lafiya an d'aura aure lafiya anci ansha taro ya watse lafiya.
Bangaren iyaye mata sun ma yaransun rawar gani dan ganin wannan shine karo na farko da suka had'a yaransu aure kuma ba tare da samun matsala ba kamar yadda sauran auren zumunci yake kawo matsala, basu san nan gaba ba wanda basa fatan hakan.
Sadeeq bai samu kansa ba daga rik'esa da abokanansa da suka yi masa murna ba har wajen karfe hudu, yana samu yana yin sallah ya shiga motarsa yaja yabar Fadar.
Bayan yayi parking ya shiga gidan shuru kamar ba kowa cikin d'akin ya tusa kansa, tayi d'ai-d'ai tana bacci hankalinta kwance, dan hijab din da tasan ma wuyan ya fita, matsawa yayi ya zare hijab din yabi gashin kanta da ya kwanto, garin zare hijab din d'ankwalinta ya zame, yayi mamakin ganin yawan gashinta irin na fulani ga cika ya tsayi, komai ya tuna ya kawar da kansa daga abinda zuciyarsa da gangan jikinsa ke muaradin kallo, a rayuwarsa yana son mace mai gashi, kwantarta yayi ya mik'e.
"Ayeeshat."
Ya k'ira sunanta da d'an karfi bayan ya zauna gefen katifar, a dan tsorace ta bud'e idonta, da hanzari ta jawo hijab nata tasa.
"Kinyi Sallah?"
Fad'in Sadeeq na zare safar kafarsa, girgiza kanta tayi sannan ta tashi ta fita alwala ta d'auro ta tada sallah bayan ta idar tayi addu'o'inta ya nemi ta kawo masa abinci data dafa, dan ya kasa cin abincin gidan auren, ita ko tsammaninta duk zai ci acan yasa ta girka abinda take so taliya da mai da yaji, wanda dakyar ta samu yajin cikin ledan doyar da daren jiya ya siyo.
Zubo masa tayi ta kawo, yamutse fuska yayi cikin had'a rai yace.
"Me wannan?"
"Abincin."
Ta fad'a tana jan baya ganin yanda yake magana fad'a fad'a.
"Yanzu wannan kika ci?"
"Eh da dadi fa."
"Dallah d'aukemin kar nayi ball dashi aka ce miki kowa irin kine baya wayewa, Mtsw."
Fita yayi a d'akin yabar gidan gaba d'aya ma, itako Ummu abincin ta d'auke ta fitar ta dawo ta zaune abinta, ganin har bayan magriba bai dawo ba nan tsoro ya fara kamata ta takure guri d'aya a haka ya dawo ya sameta bayan taci kukanta ta koshi har ciwon kai yasa mata.
Bai ko kalli inda take ba ya ajiye mata ledar hannunsa a gabanta, kayan jikinsa ya rage ya fita wanka yayi dama already yayi sallar isha'i, bayan yayi shirin kwanciya ya kallo inda take ganin yanda take k'ankame jikinta yasa yace.
"Ke lafiyarki?"
Shuru ta masa tak'i amsawa dan muryanta baya fita dan kuka, tashi yai ya nufi gurinta hawaye ya gani na bin kumatunta daga kwancen da take.
"Wani abu aka miki, ko dad'in kukan kike ji."
Girgiza kanta tayi a hankali tace.
"Kaina ke ciwo."
"Dan kanki na ciwo shine zaki hau ma mutane kuka."
"Sosaine fa."
Hannu ya d'aura saman goshinta yaji zafi rau, sai kuma yaji jikinsa yayi sanyi, d'agota yayi tana kakkaucewa ya d'aura saman katifa, ledan da ya shigo dashi ya bud'e kazane.
"Ci kad'an sai in siyo miki magani."
Girgiza kanta tayi alamar ah a.
"Kad'an fa."
"Ko naci amai zanyi."
Tinowa da jiya tilasta mata da yayi ta amayar da abinda taci yasa ya hakura ya barta badan ya so ba, kwantarta yayi lullubeta da bargo.
"Kwanta bari in nemo miki magani."
Bata ce komai ba ta lumshe idonta shikuma ya fita, chemist dake bakin hanya ya siyo mata magani ya dawo tararwa yayi tayi bacci, ajiyewa yayi ya kwanta gefenta, bini-bina duk motsin da tayi yana dubata.
Tsakar dare zazzafan zazzabi ya zuba mata ruf, ya bata maganinma yaki sauk'a, rasa ya zai yi da ita yayi da kyar ya samu ya tina wani abu, ruwa ya d'ibo da k'aramin dankwalinta ya duba cikin kayanta, dashi ya goge mata jikinta, fuskarta, cikinta, da cinyarta zuwa kafanta.
Yin haka bai dade ba yaji jikin zafin ya ragu, rufeta yayi ya kwanta gefenta motsi kad'an ya kai hannu kan goshinta, da kyar bacci ya d'aukesa ranar.

Washegari da safe karfe tara ya samu bayan ya farka yayi wanka, Allahamdulillahi ta danji sauki, Fadar Mai martaba yayi bai dade ya musu sallama duk da sauran y'an uwansa amgwayen sun so ya shiga ciki ya gaishe dasu Mami yace yana sauri, zaune ya sameta saman sallaya a bakin barenda, tashi tayi tana shirin basa wajen yace.
"Ki shirya mu koma gida."
"Yanzu." Ta tamabayesa.
"Eh." Yace da ita yana d'an harhad'a kayansa, itama shirya nata kayan tayi, bayan sun kimtsa komai suka d'auki abinda suke bukata, ya kulle gidan suka d'auki hanyar Katsina, sai da suka d'au hanya ya k'ira Mami ya fad'a mata k'iran gaggawa ya samesa daga office dan fad'anta.

Da isarsu direct asibiti ya fara biyawa, asibitin abokinsa bayan ya ganta ya rubuta mata magani suka kama hanyar gida, bayan yayi parking ya mik'a mata ledan maganin tare da jaddada mata ta tabbar tana sha, godiya ta masa ta d'auki jakar kayanta da ledan maganin ta nufi cikin gida, shima ya wuce nasa d'akin.

Yan bika kam sai da suka k'ara kwana uku kafin suka tattaro aka mik'a ko wacce gidan mijinta, kafin suka watsa, ba laifi Sadeeq ya gyara gidansa haka aka kai masa amaryarsa, da daren ranar da aka kaita ya tarkata ya d'auki komai nasa daga gidan Mami ya koma gidansa.

RAYUWAR BIEBIE GIDAN SADEEQ..

Sadaukarwa ga Ummu A'shat(Ummi Safwaan).

PhartyBb.WordPress.com

SANADIN HA'DUWARMUWhere stories live. Discover now