'KARSHE...

3.9K 187 29
                                    

NAGARTA WRITER'S ASSOCIATION

    SANADIN HA'DUWARMU
       ©Pharty BB

     Wattpad @PhartyBB
30
    Sati biyu da sunan Hauwaty, Sadeeq ya samu 'kiran Abbansu, bayan yaje nan ya sanar masa da cewa Sultaan na son Laurat da aure ya shirya jibi za suje can k'auyensu dan yin magana da manya da kuma mahaifiyar yarinya.
Da murna ya dawo gidan ya fad'a Ummu, itama tayi murna sosai.
Ranar da Sadeeq zai tafi Ummu har kuka ta masa kafin ya ce ta shirya ya kaita gidan Mami.
Bata so haka ba ta shirya cikin bak'in abaya gabansa anyi zane da ash colour, hakan yasa tayi rolling kanta da gylae karami ash colour, kwalliya tayi abinta sosai tayi kyau.

  Bayan isarsu gidan Mami, Sadeeq ya gaishe da Mami, kan ya wuce wajen Abba da Sultaan inda suke jiransa.
Daganan suka d'au hanyar k'auyen Unguwar Liman.
Bayan tafiyarsu Ummu da Mami na zaune suna hira Mami ke tambayar Ummu ina Biebie bata zo ba ko tana da aiki a office.
Shuru Ummu tayi kanta ya d'aure, Mami bata da masaniyar cewa Biebie tayi tafiya.
Maganar Mami shi ya dawo da ita hankalinta.
"Nace miki ya Biebie ko tana office."
"Mami ai..amm..Mami ai bata nan."
"Bata nan! Ina taje?"
"Tafiya tafiya."
"Tin yaushe?"
"Kusan wata uku."
"Meye!"
Shuru Ummu tayi tana zare ido.
Mami kam mamakine ya kamata, tabbas akwai abinda ke boye kuma ba mai warwaresa sai Sadeeq.
Barin maganar tayi ganin duk Ummu ta tsorata, ta kawo mata wani hiran.

  Can bangaren Abba, Sadeeq, Sultaan, karfe sha biyu suka iso, direct gidan maigari suka yada zango, bayan sunci sun sha suka gabatar da abinda ke tafe dasu.
Mutanen gurin sunyi murna sosai daga nan aka dunguma gidansu Laurat.
Abinda suka tarar shiya tsora ltasu, Abulle ke yin wanki uban tulin kaya kuma ga dukkan alamu na Dijene, ganin mutane yasa ta bari ta dauk'o ta barmu ta shimfid'a musu, Abba da Sultaan ne da mai gari da sauran mutanen suka zauna banda Sadeeq da tsaye yayi yana k'arewa gidan kallo, Can nesa dasu Abulle ta zauna.
Mai garine ya bud'e taron da addu'a daga nan ya sanarwa Abulle abinda ke tafe dasu na Sultaan na neman auren Laurat in ta amince.
Ba shawara ba tunani cikin sauri Abulle tace.
"Na bashi ita wallahi, na basa Allah yasa matarsa har a lahira."
Kallonta mai gari yayi da kyau kamar ba a cikin hankalinta take ba.
"Karfa daga baya kice kin fasa."
"Ah a Maigari na bashi ita, ga Yayan Mahaifinta na bashi ita ya zartar da duk hukuncin da ya dace a kanta."
Fad'in Abulle na nuna Abban Sadeeq.
"To Allahamdulillah."
Fad'in Mai gari, anan Sultaan ya bada sadaki dubu hamsin da sauran kud'ad'en da ake bukata aka saka rana wata hudu in da Abba ya zama wakilin Laurat Sadeeq ya zama Wakilin Sultaan, nan aka damk'awa Abulle kud'in auren Laurat da komai da komai.
Anan Abba ya sanar mata ba anan za a d'aura auren ba acan gidansa za'a d'aura, in biki saura wata daya zai turo a d'aukota, nan ya kara bata wasu kud'aden ta rik'e a hannunta.
Kuka wiwiwi Abulle ta saka tana rokon gafararsu dan ita kad'ai tasan rayuwar da ta shiga bayan gudowar Dije daga karuwanci.

  Bayan sun gama komai suka d'auki hanyar komawa gida.
Da isarsu bayan sun huta sunyi wanka sunci sun sha, Abba ya sanar dasu an tsaida ranar d'aura aure nan da wata uku, Mami ta taya su farin ciki inda anan ta d'auki waya ta dinga k'iran yan uwa tana fad'a musu.
Har dare Ummu da Sadeeq na gidan kafin suka musu sallama zasu tafi, anan Mami ta tsare Sadeeq cewar ina Biebie.
Kansa a 'kasa da kyar ya furta.
"Na saketa Mami."
Ba Mami ba hatta Ummu sai da ta tsorata d'an cikinta ya juya.
"Saki kuma Sadeeq! Meya faru? Tukun ma saki nawa ka mata"
"Saki d'aya."
Ajiyar zuciya Mami ta sauke jin saki d'aya ya mata kan tace.
"Sadeeq in har kana nemawa kanka samun kwanciyar hankali daga wajen Abbanku gobe kaje kayi bikonta tinda saura wata d'aya ta gama Iddah."
"Mami amma..."
"Shit umarni na baka, tashi ka fitamin a d'aki."
Tashi yayi ya fita Ummu tabi bayansa sum sum, duk ta tsorata da Sadeeq.
Bayan isarsu gida daren ranar da kyar ta yarda masa gani take itama daya samu abinda yake so daga wajenta zai saketa.
Washegari haka yabi umarnin mahaifiyarsa da dare yaje bikon Biebie, inda yasha fad'a da nasiha wajen Mommynta, dan ita kanta tasan halin 'yartan.
Jin Sadeeq yazo yana nemanta a falon baki da gudu ta tashi zata fita, Mommynta ta daka mata tsawa.
"Haka zaki je masa kamar wacce aka sallamo daga gadon asibiti."
Sai lokacin ta kalli jikinta, dogon rigane sai 'karamin gyale data d'aura, tayi fari ta rame sosai dan tin lokacin da Sadeeq ya kawo mata takardar saki ta rasa isasshen lafiya har office daina zuwa tayi.
D'akinta ta wuce ta shirya cikin leshi mai kalar sararin samaniya, heavy makeup tayi ta feshe jikinta da turare ta fita.
Falon baki tayi anan ta tararshi zaune, gefe ta zauna kusa dashi kad'an dan ita yanzu tsoro yake bata.
"Ina wuni."
Tace dashi tana wuk'i wuk'i da ido.
"Lafiya, ya kwana biyu."
"Lafiya."
Shurune ya biyo baya, ganin lokaci na tafiya yasa Sadeeq mik'ewa.
"In kin shirya tafiya mu tafi ko."
Kallonsa tayi kamar za tayi kuka, amma Sadeeq ya mugun raina mata hankali.
Tashi tayi ta fita, shima fitan yayi.
Sai da tasha kukanta kafin ta shirya ta fito tama Mommynta sallama inda ta mata nasiha mai ratsa jiki ta fito.
A cikin motar ta samesa ta bud'e ta shiga yaja suka bar gidan.
Da isarsu gidansa bayan yayi parking sun shigo fakon ya tarar Ummu na zaune tana kallo, ta juya kofar shigowa baya, kusa da ita ya k'arasa ya zauna tare da rikota yana kaiwa wuyanta kiss.
"Ya kike, ya Babyna."
Murmushi tayi tana 'kara kwanciya jikinsa dan kwata-kwata bata kula da Biebie dake tsaye ba, tace.
"Lafiyarmu lau."
"Muje inyi wanka please dan yunwa nake ji."
"To Yayana."
Tace tana tashi shima ya tashi suka wuce side nnata, Biebie kam ganin abin yafi karfinta yasa ta wuce side nata tin kan su tashi.
Bayan Sadeeq yayi wanka ya nemi ta kawo masa abinci d'aki, anan suka ciyar da junansu, bayan sun gama ta fitar da plate din ta dawo itama tayi wanka tayi shirin bacci suka bi lafiyar gado.

   Sai washegari Ummu taga Biebie, anan suka gaisa har Biebie na neman gafararta akan abubuwan da ta mata, nan Ummu tace mata ba komai ta yafe.
Tin daga ranar rayuwar ma'auratan ya sauya, sun shimfid'a rayuwarsu cikin so, kauna, yarda, aminci da yardar junansu, a haka Ummu ta samu gurbin karatu a jami'a inda tske karantar Islamic History.

    Bayan wata Uku.
Yayi dai dai da ranar auren Sultan da Laurat, Sadeeq yana ji yana gani Ummu da Biebie suka had'a kayansu suka tafi gidan Mami.
Tin ana bikin saura wata d'aya kamar yadda Abba yace haka yayi ya tura Driver ya d'auko Abulle da yayanta Dije da Ja'afar, gaba dayasun sun nutsu sun ma kansu karatun nutsuwa, dan yanzu suna ganin sakyayyar muguntan da suka ma marainiya Ummu wacce yanzu suna ganin ishara.
Tin ran talata suka fara gabatar da shalin biki, har ranar asabar da aka d'aura aure aka mik'ata gidan mijinta.
Ummu tin da taje bata aikin komai ahlin gidan sun hanata ganin cikinta ya girma, sai dai a dafa a zubo mata taci a d'auke, wanka ke 'dagata daga inda take, ko wani lokaci Sadeeq na kiranta ya lafiyarta dana Babynsa, sai dai tayi murmushi tace, lafiyarsu lau.
Bayan angama biki kowa ya watse banda Ammin Ummu data zauna har lokacin haihuwar Ummunta.

   Wata biyu da sati biyu wata Safiyar Asabar Ummu ta tashi da nakuda, da taimakon Biebie da Sadeeq suka kaita asibiti basu dad'e da zuwa ba awa biyu ta haifo d'an ta santalele dashi sak Mahaifinsa, fari mai yalwar gashi.
Haihuwarta da awa d'aya asibitin ya cika da  yan uwa da abokan arziki dan murnar zuwan jariri.
Ganin lafiyarta da abinda ta haifa yasa likita sallamarta suka koma gida.
Cikin kwanakin kafin suna taga gata da soyayya wajen mijinta da yan uwa, abinda Biebie ke mata kuwa har ya zarce tunanin mai tunani dan kowa mamaki yake, itace ta tsaya mata kan komai.
Ranar suna yaro yaci sunan baban Ummu Muhammad suna 'kiransa Safwaan, kowa yayi murna da haka musamman Ummu da Amminta harda d'an guntun hawayensu na tino musu dashi a kayi.
Watan Safwaan takwas Biebie ta haihu itama 'yarta mace taci sunan Mami suna k'iranta Afnan.
Haihuwar Biebie da wata Uku Rahma ta haihu y'a mace itama.
Ana washegari suna Biebie ta tafi zata kwana, 'kiri 'kiri Sadeeq ya hana Ummu tafiya da fushinta ranar ta kwana.
Da safe kuwa karfe takwas ta gama ayyukanta ta fito kofar falon tana jiran Sadeeq ya fito, tama Safwaan wanka ta shiryashi cikin riga da wando rigar mai layin lime da sea blue wando levender colour haka safar kafarsa lime colour.
Ita kuwa ta shirya cikin dogon riga na atamfa mai blue da brown tayi amfani da brown gyale.
Rikota ta baya Sadeeq yayi bayan ya karbi Safwaan da hannunsa na hagu ya shirya cikin yadin kashmir dark blue, yasa bakin takalmi da agogo.
"Kinga yarona ya fara hakori yana ta kokarin kai hannunsa baki."
Hannu Ummu ta kai bak'in Safwaan, cizo yasa mata duk da ba hakorin sai alamar fitowa, hakan yasa ta bud'e baki, shiko Sadeeq dariya yasa musu.

   Ganin zasu bata lokaci yasa Sadeeq yin gaba, tabi bayansa suka shiga motar yaja.
A kofar gidan Rahma yayi parking ta masa sallama ta fito ta wuce cikin gidan sunan.
Anyi taro suna lafiya, an fara lafiya an gama lafiya, aka watse lafiya, Sadeeq shi yazo d'aukan matansa suka wuce gida.

  Da daren ranar gaba d'aya, Sadeeq, Ummu, Biebie, Safwaan da Afnan suna zaune yaran wasansu suke, iyayenko hira suke yi abinsu.
Nan Sadeeq ya kallo matansa yana d'aga musu gira.
"Matana yafa kamata yarannan su samu k'anne."
Tashi Biebie tayi ba shiri ta d'auki y'arta.
"Ba da ni ba haihuwa yanzu sai y'ata tayi shekara hudu."
Tana fad'ar haka ta kama hanyar side nata, kallonsa Sadeeq ya mai da kan Ummu.
"Ke fa Wife, kema sai Safwaan ya shekara hudu."
Tashi tayi ta d'auki Safwaan tana murmushi.
"Ni sai ya shekara tara a na goma na haifo masa k'ani ko 'kanwa."
Dariya Sadeeq yayi yana bin bayanta.

Asubabi ta Gari Mr and Mrs Abubakar Sadeeq.

            Taimako.
  Ka taimaki mutum ko da baka san asalinsa musammam in yana cikin tsananin bukatar hakan, ko dan gudun fadawarsa ga halaka.

  ALLAHAMDULILLAH
             TAMMAT BI HAMDULLAH.

  SADAUKARWAR NAKI NE UMMU A'ISHAT MUHAMMAD (UMMI SAFWAAN), ALLAH BAR KAUNAR DAKE TSAKANINMU, ILYSM.

   

PhartyBb.WordPress.com

SANADIN HA'DUWARMUOù les histoires vivent. Découvrez maintenant