Part 1 page 136-140

295 20 0
                                    

 *LABARIN RAYUWAR*

*Asma'u Husnah*


Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*


🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*


Dedicated to *My Lovelly Momy*
*Momy nah a koda yaushe addu'a ta bazata taba karewa gareki ba.*

*Kece komai nawa. Ina nufin komai fa.*

*Masoya a ko da yaushe kune silar dariya ta. Bama in ina karanta comment din ku.*

*To Alhamdulilah Da soyayyar ku a gareni. Allah ubangiji ya bar ni da ku.*

*Gaskiya ina jin dadin yadda kuke bibiyar labarin nan.*

*Masoyan Aslam*
*Masoyan Sabir*
Kuna ina ne?



*136-140*

An Kar6o Daga *Anas (ra)*, Lallai *Manzon Allah(ﷺ)* Yace: *“Idan Aka Gabato da Abincin Dare, to Ku Fara Dashi Kafin Ku Sallaci Magariba”*. (Bukhari da Muslim)_




Suna zuwa asibiti aka amshe shi. Sun jima akan sa dan har akai sallar asuba.

Sallah Asma'u tayi ta jima tana wa Dady Addu'ar Allah ya bashi lafiya.

Dady kuwa ganin jikin sa sai wasiya yake bayar wa yana cewa,
"A kira masa *Husnah* ku kira min matata da 'da na da Auta tah *Husnah* "

Da sauri Dr ya karasa ya kira su. Asma'u na shiga da gudu ta karasa wajen Dady ta rike hannun Dady tana jijigawa tana cewa
"Dady gani. Dady ga *Husnah* ka."

Dady dake kwance yana fitar da numfashi sama sama, ya kalli Mami da Buhari. Ya ce
"Amina Allah miki albarka. Allah ya baki aljanna madauka. Buhari kai ma Allah maka albarka Allah ya saka a gidan aljanna Allah baka mace ta gari."

Ya karasa maganar da kyar. Cikin sa ya kara rikewa ya kalli Asma'u ya sakar mata murmushi ya ce,
"Ga *Asma'u Husnah* nan ku kula da ita. Ita ce, yarinyar karama kar ku bar ta tai kuka. Amina Allah miki Albarka. *Husnah* Allah ya miki albarka. Allah baki zuri'a ta gari Allah ya saki a Aljanna."

Hannun Buhari ya kamo tare da na Mami. Kallon Asma'u yayi ya sakar mata murmushi.

Kalamar shada ya dinga fadi a hankali. Mami ita take tayasa amsawa. Su Asma'u da Buhari kuwa gaba daya sun rikice da kuka.

Can Dady ya saki hannun su idon sa ya lumshe, cikin firgice, Mami ta kwadawa Dr kira.

Dr ne ya shigo ya duba shi. Kai ya girgiza kawai.

Kallon sa Asma'u tayi ta ce,
"Dr ya jikin nashi ne?"

Kallon su Dr yayi ya ce,
"Sai dai kuyi hakuri Allah ya amshi rayuwar sa."

Asma'u dake tsaye wata juwa taji tana dibar ta. Daga nan duhu ya rufe mata idon ta.

Zubewa tayi a kasa. Mami ma faduwar tayi. Buhari kuwa ya rasa ya za yi.

Da sauri Nurse suka yi wani Daki aka kai Mami da Asma'u aka kwantar da ita. Suna kokarin ceto rayuwar su.

Buhari kuma ya buga waya ya fadawa Uncle Abubakar kanin Dady da uncle ilyasu da kanwar sa.

Sai Momyn Aslam da sauran yan uwa. Cikin minti kadan gida ya cika da jama'a.

Mami da Asma'u kuwa suna Asibiti. Momyn Aslam a lokacin suka taho a jirgi.

Karfe sha biyu aka sa za ayi jana'idar Daddy.

Momyn Aslam na zuwa, ta zarce asibiti. tana zuwa Mami ta farka.

Rayuwar  Asma'u Husnah 1 & 2 Complete ✔Where stories live. Discover now