Part 2 page 1-5

345 24 0
                                    

*LABARIN RAYUWAR*
  *Asma'u Husnah*

*part 2*

Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*

Dedicated to *My Lovelly Momy*

*Bismillahir Rahamanir Rahim*

*Alhamdulilah.*
Allah nagode maka da ka bani ikon fara cigaba da karashen littafin *Asma'u Husnah* Allah ina rokan ka da ka bani ikon kammala shi lafiya kamar yadda na fara lafiya.

Masu korafi akan littafin kucigaba da bibiyar sa zakuyi komai.

*Mahaifiya ta farin cikin rayuwa ta. Mahaifiya ta hasken idaniya ta. Allah dada lafiya da nisan kwanan Momy Ameen*

Allah ka jikan *Mahaifina, da dukkan musulmai baki daya.

*Kannena farin ciki na. Allah bar min ku. *Nusaiba and Hauwa'u (Yasmeen)*
One love.

Ina mika gaisuwa ta ban girma gare ki yar uwa Anty nah. *Rashida Abdullahi Kardam* Allah ya dafa Allah ya karawa Mama lafiya. Allah baki miji nagari da zuri'a daiyaba. Ameen.

Sai sakon gaisuwa ta ga *Hajiya Nafisa* Momyn mu. Allah ya kara girma ya kara lafiya da arzuki ya Allah ya raya zuri'a. Ameen.

Sai gaisuwa ga Dukkan nin yan uwa marubuta musam yan kkungiyar HAJOW tare da yan uwan abokan azurki masoya. Allah ya kare mana ku Ameen.

Masoya nagode da kaunar ku a gareni nima ina kaunar ku.

Allah marasa lafiya na gida dana asibiti Allah ya basu lafiya. Allah ka daukaka musulunci da musulumai. Allah ka karya kafirci da kafirce.
*Ameen*

Bari mu shiga cikin karashen littafin dan muji abinda zai faru.



*1-5*



Ganin halin da Aslam. ya shiga ba karamin dagawa Dady hankali yai ba.

Amman duk da haka ya ce bai yadda Aslam ya auri Pretty ba.

Aslam kuwa ba karamin tashin hankali ya shiga ba. dan jinin sa ba karamin hawa yayi ba.

Momy da batasan me yake faruwa ba yasa ta shiga tashin hankali na rashin ganin Aslam ba.

Dady ta tara dan ganin bata ga Aslam ba har dare.

Dady ne ya fada mata duk abinda ya faru.

Momy mamaki ta tsaya yi yanzu abinda Aslam ya zaba kenan.

Zama Momy tayi ta dafe kan ta. Dady ne ya zauna kusa da ita ya kamo hannun ta.

Kallon sa tayi idon ta jajir ta ce,
"Dadyn Aslam ya zan yi da Asma'u. Kai kan ka shaidane akan soyayyar dake tsakanin su. Ban san me ya samu Aslam ba har haka ta faru. Amman ka min izini gobe na tafi kano naji me yake faruwa."

"Ba komai. Ki kwantar da hanaklin ki. Na amince kije Allah ya kyauta."
"Ameen!"

Kwana Aslam yai a asibiti dan Dady ko wajen sa bai koma ba.

Sai Pretty ya kira ya ita ta kwana a wajen sa.

Washe gari Momy ta daga zuwa Kano.

Asma'u ce kwance zazzabi ya rufe ta dan jikin ta kamar wuta.

Sai rawar sanyi take, idanun ta sunyi jajir dashi.

Mami ce ta shigo dakin rike da wani dan bowl da karamin towel a hannun ta.

Zama tayi a gefen Asma'u ta yaye bargon da ta rufa dashi.

Hijab din jikin ta ta cire mata ta matsa kusa da shi ta na tsoma towel din a cikin ruwan ta dauko ta matse sannan ta saka mata ajiki.

Rayuwar  Asma'u Husnah 1 & 2 Complete ✔Where stories live. Discover now