13

510 33 0
                                    

*NAYI DACE*

Maryam💕
Wattpad@mamsuhaimerh

*💫DA BAZAR MU WRITER'S ASS💫*

*We are here to make you happy, smile and to réalized that we are the best among all......DA BAZAR MU MUKE TUN'KAHO.*

13
        Zuru zuru nayi cikin tsananin kunya da takaici na tashi nayi hanyar fita, hannuna naji an ri'ke na juya naga sultana

"Ke Kuma sha-sha-sha da bakisan ciwon kanki ba, ta rabaki da saleh ta aureshi amma kina nan kina ma'kale mata, sai kace mayya,ke dai lalacewa ta tabbata a kanki wallahi, kuma kina nuna mata soyayya bakisan hakan 'kara sanya mana tsanarta yake ba "

Janye hannuna nakeso nayi amma ta 'kan'kame, cikin fad'a tace

" Wai meyasa kuke haka ne? Meyasa bazaku ja girmanku bane? Yanzu menene amfanin hakan da mukeyi please, na fad'a muku 'karya nake amma bari na fad'i dalilina na yin hakan"

Sakin hannuna tayi tace " Ina sane na had'a wannan 'karyar domin raina na min dad'i idan naga kuna mata haka "

Banyi wani mamaki ba da jin hakan, domin na dad'e ina jin rashin yarda da sultana a raina, komawa tayi ta zauna ta juya min baya tace

" Bayan nayi hakan kuma na sami nutsuwa a raina sai ya usman ke nunamin bayaso ina yin hakan, kenan Ina ri'ke da soyayyar saleh bayan ina aurensa, kenan auren nasa baida amfani, idan kuna ganin ina sonta ne ni ba haka bane, kawai ni nawa hanyar hukuncin ta banbanta da naku ne, idan kunga zaku ci gaba da zubda girmanku a haka......"

Fita nayi kaina na juyamin, ina shiga gida na fara hawaye, Kan kujera na kwanta ina kuka mai cike da takaici, duk halaccin da nayi wa sultana da abinda zata sakamin kenan?

Alamun ana bud'e gida naji ban ko motsa daga inda nake ba, ina jinsa ya shigo ya 'kwan'kwasa 'kofa alamun naje na masa welcome

Da ya tabbatar bazan fita ba da kanshi ya shigo, cikin damuwa ya ajiye ledar hannunsa yace

"Me ya faru "

Cikin shesshe'kar kuka nace

" 'yan uwanka sunyi min gorin haihuwa, dan Allah boo-boo muje asbiti a dubani domin su tabbatar lafiyata 'kalau, sun'ki bani babyn wai naje na haifa nidai muje asbiti kawai...."

Kwantar dani yayi a jikinsa yace

" Haba my boo, ke kika ce kin dena damuwa da abinda 'yan uwana zasu ce miki, yanzu ko munje asbiti za'a ce munyi garaje ne aurenmu baiyi shekara guda ba fa har yanzu, sunyi hakan ne dan kiji haushi kamata yayi ki nuna musu baki damu ba, my boo ni nake aurenki ba su ba, kuma ni ban shirya gintse amarcinmu a wannan 'kan'kanin lokacin ba, sannan haihuwa ta Allah ce, su d'in su suka haifi kansu ne? ki rabu dasu karki sake zuwa gidan sai ranar suna shima karki zauna "

Ban amsa masa ba yaci gaba da rarrashina

"My boo nifa ban sanki da mita ba, nifa kukannan naki ban gane masa ba, ba dai kukan rashin ganin baby bane? to gata nan d'ago kanki ki kalleta "

Mi'komin wayarsa yayi naga pic d'in jaririyar, mi'ka masa nayi na kwanta a 'kirjinsa ina had'iye sauran kukana, ko me sukamin ni naja tunda nakai kaina cikinsu  kaman wata tsiyar zasu min bayan nasan had'uwata dasu bata zama alkhairi, yanda saleh yace bazan sake nufarsu ba sai suna, shima bazan zauna ba zan taho

Share haihuwar nayi a kwanakin na shiga harkata, saidai jaririyar ta tsayamin a raina sosai nakeso na ganta, amma tafi 'karfina.

Ranar suna da wuri na shiga gidan na tafi da kayan barka na, diaper bag na Kai mata da set uku na kayan jarirai da atamfa d'aya.

NAYI DACE.Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang