BAHAGON LAYI BABI NA 13&14 DA 15&16

71 8 0
                                    

[8/5, 09:59] Hassana D'an Larabawa🥰: *TYPING*📲

🏘️ *BAHAGON LAYI* 🏘️

             (A RAN GAMA)

*TARE DA ALK'ALAMIN*✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR*👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI

         *DA KUMA*👇

BAHAGON LAYI


*BABI NA SHA UKU DA NA SHA HUD'U*

✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️

✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

           

______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________

https://www.facebook.com/groups/1533639276725

*INA YIWA D'AUKACIN AL'UMMAR MUSULMI BARKA DA SALLAH,DAFATAN KOWA YAYI SALLAH LAFIYA*👏🥰

       *GA SAK'O DAGA MATAN BAHAGON LAYI,SUNCE NA SANAR MUKU KOWA YA K'ULLO NAMA YA BANI NA KAI MUSU,HARIRA KUMA TANA YIWA WAD'ANDA SUKA JE KITSON SALLAH WAJENTA BANGAJIYA,DAFATAN WARIN DA SUKA SHAK'A BAI KUMBURA MUSU CIKI BA*?😂😂😂




Jikinta ya kama karkarwa k'afarta na rawa,tuni idanuwanta suka ciko da hawaye saboda ta san Mahaifinta ba yayi mata da wasa,kallon da yake mata kawai a yanzu haka ya isa yasa hantar cikinta kad'awa.
Malam Ya maida kallonsa kan Salisu yace.

"Idan akwai mukulli a hannunka bud'e mu shiga"

Salisu cikin sunkuyar da kai ya amsa da "To Malam" Sannan yasa makullinsa ya bud'e gidan.

Malam ya kalleta fuska a d'aure yace.

"Zo ki shige mutuniyar Banza,kina yawo k'afa kamar kwarkwaro"

Jikinta na rawa ta rab'a ta shige tana Hararar Salisu ta k'asan idanuwanta.

Suka bita a baya har zuwa cikin gidan,tana niyyar bud'e d'akin nata Malam ya daka mata tsawa da cewa.

"Dawo nan Dan ba shiga d'akinki zan yi ba,Mara kunya fitsararriya"

Ta dawo tana sosa kai ta tsuguna,yayin da Salisu ke tsugune shima kansa a sunkuye,cikin matuk'ar b'acin rai Malam ya soma yi mata fad'a.

"Ba k'aramin mamaki kike bani ba Saratu,Mamakin bai wuce na watsar da kyakkyawar tarbiyyarki da kika yi ba kika aro mummuna kika yab'awa kanki,Allah shine shaidata na baki tarbiyya ta gari na baki ilimi na addini Wanda zai miki jagora zuwa bautar ubangijinki da bautar aure,amma a yanzu duk kin watsar babu abin da kike yi sai zaluntar mijinki da munana masa,tun yana hak'uri dake har kin kaishi mak'ura yazo ya sanar dani komai,Saratu kin san yawan zunubin da mace ta ke samu idan ta sake ta fita ba tare da izinin mijinta ba kuwa?kin san yawan zunubin da mace take d'auka akan wulak'anta miji da lek'e idan baya nan?Saratu idan baki yi tunanin ta nutsu ba zaki kai kanki wutar jahannama,mace tayi biyayyar aure tabi Allah da manzonsa ma amma Allah yana jarrabarta balle ta k'etare dokokin sa,kiyi duba ga mahaifiyarki ta zame miki izna a rayuwarki,tabi Allah da manzonsa ta tsare hak'k'ok'in aure yadda ya kamata,ta kasance mace mai bin umarnina da yi min biyayya da kaucewa b'acin raina,amma duk da hakan Allah ya d'ora mata lalurar da ko tashi zata yi sai an d'agata,to ke da kike k'etare iyakokin Allah da na aure idan Allah ya tashi jarrabarki kin san wace irin jarrabawa zai miki?Ba yau na fara yi miki nasiha da fad'a akan munanan halayen da kike ba,amma inason in shaida miki wannan ne na k'arshe,Annabi (S A W)ma ya umarci d'iyarsa Fad'ima (R A)tayi wa mijinta sayyidina Ali (R A)Biyayya,duk da kasancewarta mai girma d'iyar masu girma,ba ke ba karankad'a miya tasono dake,Annabi (S A W)yace"Da Allah zai umarci wani yayi wa wani sujjada,to da ya umarci mace ta yiwa mijinta sujjada"Saboda tsananin girman miji a wajen matarsa,Dan haka ki maida hankalinki Saratu,wannan ita ce hanyar aljannarki,domin aljannar taki tana k'ark'ashin k'afar mijinki,wallahi tallahi idan kinga kin shigeta to sai dai idan ya d'aga miki,to ta ya ya zai d'aga miki kina cutar dashi kina zaluntarsa?ita zuciya ai an halicceta ne ga son Wanda yake kyautata mata,haka nan ga k'in Wanda yake munana mata,duk randa kika yi sake ragowar k'imarki ta zube a idanuwan mijinki kin kad'e Saratu,domin ba zaki tsira da komai ba,kuma ko a lahira ni kaina mahaifinki ba ruwana dake,Dan haka ina yi miki nasiha da kiji tsoran Allah,ki sani Allah yana kallon dukkan abin da kike aikatawa,maganata dake ta k'arshe ita ce, Muddin kika sake Salisu ya gaji da halayyarki ya koroki gida ya sake ki to fa tabbas zaki d'and'ana kud'arki,ba zan koreki a gidana ba saboda ni Mahaifinki ne,amma wallahi zaki gwammace zaman kurkuku da zaman da za kiyi a gidana,wannan ce maganata dake ta k'arshe,ya rage ruwanki ki gyara ko ki cigaba da aikata munanan halayenki,(Imma shakiran,wa imma kafura).

BAHAGON LAYIWhere stories live. Discover now