page 18

351 25 0
                                    

LA L A T A  [18]

Writing By: _SADNAF_

Copy ALBISHIR NOVELS
Whatsapp number 08163840712



bazan kara kira ba amma zan San yanda muka hadu,dan nasan tasleem nasona bazan sha wuyan shawo kanta ba,tasleem shigowa dakinsu tayi bayan ta gama taya Umma gyara, tazo ta samu Fatima na jijiga kai tana huci, ke kuma lafiya keda waye, hmm nida dan akuya izzadeen, bangane ba kiranki yayi awaya na zana mishi DDC,kinyimin dai dai dan iska ko mai zai cemin daya kira,rabu da shege,har yanada gut din kara kiranki,wlh da dazu kun barni na mishi kaciya da sai ya manta sunanki ballantana har yayi tinanin kiranki,ba matsala ai tunda kinci ubansa,yauwa dazu muna maganar kayan daza Mu sa....


       akwana atashi babu wuya abban Yusrah sunje sun tamabaya wa el Bahrain auren tasleem, anyi komai cikin mutunci da mutuntawa, inda aka sa rana sati uku bayan bikin el Bahrain da Yusrah, abbansu tasleem dai bahaka yaso ba, yaso tasleem ba mai mata ta aura ba, laakari dayayi da irin hallitar tasleem amma ganin ta gabatar dashi amatsayin Wanda zata aura yasa yasanya musu albarka, yau ake kamun Yusrah agidansu el Bahrain kasancewar filin gidan nasu babba ne anan akayi decoration,aka kawata gurin,amarya tasha kyau ba kadan ba,dan ummansu el Bahrain ba karamin gyara tasa akayiwa Yusrah ba dan abbansu el Bahrain yasaki kudi sosai,bangaren el Bahrain kua siyayya yayi wa tasleem da Fatima na bikin,inda suka nuna jin dadinsu,kwalliya mashida da Fatima sukaje sukayi,suka sa wani atamfa ja da baki anyi mishi fited gown bakaramin kyau sukayi ba,humra da turaren wuta Umma tasa akayo mata Daga maiduguri,mai uban yawa tasa akai wa yusrah,tasleem ma ba abarta abaya ba kulolli tasiya masu tsadan gaske set uku,tabawa su Fatima sukai dan tace batasan zua kamun,sabida agidansu el Bahrain zaayi,kuma tana kunyar aringa nuna ta amatsayin amaryar da el Bahrain zai aura dan bayan ansa ranar su da el Bahrain taje ta gaida hajiyar el Bahrain haka taringa sawa ana kiran danginsu nakusa su zo su ganta shiyasa bata San zua,haka Fatima da mashida sukat dungunzuma da uban kaya suka dau hanyar gidansu el bahrain,akofar gidan aka saukesu,aka sauko musu da kayan, suka sa almajirai suka shigar musu da kayan suka bi bayansu,en mata suka yi ta wucewa dagani kawayen Yusrah ne,dan duk sa,anin Yusrah ne,girgiza kai Fatima tayi friend kinga low class girls dinan yanda suke rawar kai wai suma sun girma,kai habibaty ina laifi sunyi kyau fa,umm karma su daukau mu sa,aninsu ne aa yaushe ido ba mudu ba  ai yasan kima,ahaka suka karasa palon su el Bahrain dake cike da mutane,hajiyarsu el Bahrain nazaune acan gefe,karasawa sukayi gabanta suka zube akasa suka gaisheta,ta amsa da faraa afuskarta ta tambayesu ya tasleem bata zo suka Ce batajin dadi ne,amma zatazo gobe,suka bata sakon da Umma da tasleem suka Bawa Yusrah ta amsa tana godiya tare da Zabga musu adduoi,suka tambayeta ina Amarya,tasa aka rakasu inda Yusrah take.

         Wani bangare aka kaisu agidan anan Yusrah take zaune da kawayenta,ana mata makeup,amma gama mata gwagwaro ake nada mata,material ne ajikinta Riga da skirt,skirt din  Daga kasa yadan bude purple da flowers din baki da aka jejera askirt din,kasancewarta fara kayan sun karbeta sosai, sallama sukayi gabadaya en dakin suka juya suka amsa ciki harda Yusrah fuskarta dauke da murmushi,Anty Fatima sanunku da zua,Fatima kua ganin duk saoin Yusrah ne adakin yasa ta amsa ayangance suka kame agefen gado,yauwa Amarya kinsha kyau gaskia Fatima tace tana murmushi,sunkuyar dakai tayi nagode aunty Fatima,ya aunty tasleem bata zo ba,wlh  bata dan jin dadi amma karki damu gobe zatazo,Allah yakaimu,wata mata Ce ta leko dakin,en matan Amarya yakamata kufito haka ana ta jiranku,kun bar mutane azaune,mikewa kawayenta sukayi gabadaya,mai makeup din ta kara gyarawa Yusrah zaman gwagwaron,suka saka Yusrah atsakiya,kallon su amarya, tayi aunty kuzo mutafi,karki damu zamu biyoku abaya,to tace suka fita Daga dakin,mashida kallon Fatima tayi habibaty gaskia Yusrah tayi kyau,uhmm ba laifi kam tayi kyau tashi muje,in mata hotuna inturawa aunty tasleem kinsan tace in mata hotuna,fita sukayi farfajiyar gidan inda aka jejera kujeru dan azauna,Amarya Yusrah na zaune akujerar amare sai sparkling take kamar star,gefe daya kuma mai kidan asharalle na zuba kida,gaskia gurin ya kawatu,manyan kawayen ummansu el Bahrain ketayiwa Yusrah yayafin kudi duk da ba rawa take ba tana Daga zaune sai sunkuyar dakai datakeyi dagani kasan kunya takeji,wani net aka dauko mai uban kyau aka rufeta,wata tsohowa tazo ta bude ta,ta fesa mata turare,aka saki gudah,Fatima da mashida sai video suke dauka awayarsu,dakyar aka bar Yusrah tashigo filli dan ta taka rawa,dan gabadaya en uwa da abokanan arziki,rubdugu suka mata suna mata hoto, tana shiga filin mashida ta bude Jakarta tazaro bundle din ashirin ashirin guda hudu tabawa Fatima biyu ta dau biyu suka shiga fillin suka fara mata liki,Yusrah dai na kame aguri daya,ko dan motsa jiki batayi,ahaka sukayi hotuna da ita,suka dauke ta ita kadai,suka bar fillin,suka koma gefe daya suka zauna,ahaka aka gama kamun inda akayi rabon abubuwa mai yawa,dan duk wanda yayi attending bikin yasamu,har dasu agogo mai dauke da  hoton ango da amarya,su Fatima sai da aka kuma ware wasu na musamman aka basu,ana kiran sallar magrib aka dakatar da kida,wasu suka tafi wasu suka tafi suyi sallah su dawo,acikn wayanda suka tafi harda su Fatima,inda drivernsu mashida yazo yadaukesu,yafara sauke Fatima agida sukuma suka wuce,tana shiga gidan Umma ta Tarar apalo ta mata sannu da gida,kun dawo, ee,ina mashidar sun wuce gida,umma hajiyarsu el Bahrain tace agaisheki amiki godiya,haba me abin godiya,Umma wlh bakiga yanda kamun yahadu ba bari ma kigani,hotunan tafara nuna mata, bayan tagama nuna mata tashiga video nan ma ta nuna mata videon data dauka,kai masha Allah Abu yayi kyau Amarya tayi kyau sosai,Umma shiyasa nakeso ayi organising na aunty tasleem haka,kedai kiyi addua Allah ya ara mana tsawon rai da Nisan kwana ameen Umma,ina aunty tasleem ne,tana daki dazu ma ta karbo muku dinkin dazakusa gobe, mikewa tayi yauwa ta kyauta bari naje na gwada inga ko zaimin kyau dan gaskia gobe sonake na bada assignment,ta nufi dakinsu,tura kofar tayi da sallama tasleem ta amsa ta cigaba da wayar datakeyi,ganin haka ne yasa ta dauko kayan datake tunanin shine Wanda tasleem ta karbo ta zazzage akasa,waw gaskia dinkin nan yayi kyau tace tana Daga.   wa,sallama tasleem tayiwa el Bahrain da suka kusa awa daya suna waya, sis ajiye kayanan kizo kibani labari, Aunty bari na gwada dinkina nazo nabaki labari, aa dan Allah zoki ban labari anjima kya gwada,kan gadon Fatima tahau,tabude mata hotunan,data dauki Yusrah,sakin baki tasleem tayi tana kallon hotinan,gaskia sis Yusrah tayi kyau ba kadan ba,huuh idan el Bahrain yaganta ai ji zaiyi yadaina sona,sabida me Fatima tace tana yatsina fuska,bakiga kyaun data yi bane,

LALATAWhere stories live. Discover now