L A L A T A [31]
Writing By: _SADNAF_
Copy ALBISHIR NOVELS
Whatsapp number 08163840712Tasleem kua el Bahrain naja mata kofarta ta rushe da kuka,wani kishi da bakinciki daya lullubeta,namiji munafiki,wato inya zo gabana sai ya tsarani inyaje gaban Yusrah sai ya tsarata, haka tyi ta magana ita kadai,sai data ga surutan datake ba amfani zai mata ba yasa ta rufe ido tafara karatun qurani ji tayi zuciyarta namata sanyi ahaka tayi ta karantun har bacci yadauketa,kiraye kirayen sallahr asuba ne yatashi el Bahrain Daga bacci yamike yaje ya dauro alwala,yazo yatashi Yusrah,ta Mike dakyar itama tayi bandaki,fita yayi Daga dakin yanufi bangaren tasleem dan ya tasheta tayi sallah,yana tura kofar yaga tasleem azaune akan sallaya,tana Jan carbi ko dagowa batayi ba,dan tasan shine,wani irin haushinshi takeji,shikuwa ganin bata dago ba yasa yakoma dakin Yusrah yaje ya tarar itama tayi alwalar tana kokarin sa hijabi,kusa da ita yje ya tsaya deserved one, ya jikin naki yace yana taba wuyanta,dasauki tace tana sunkuyar dakai dan wani irin kunyarshi takeji,deseverd one jiknki har yanzu da zafi,bari in gari ya waye mutafi asibiti arubata miki magunguna,yaya naji sauki fa kawai dai jikin nawa ne dazafi,aa zamuje bari natafi massalaci inadawo insa ma miki Abu kici sai mutafi,yajuya yatafi massalaci,Yusrah kuma ta hau kan sallaya ta tada sallah,el Bahrain na dawowa Daga massalaci ya cire doguwar rigar jikinsa,yatafi bandaki yadauko zanin gadon daya cire,yafara wankewa sai daya tabbatar stain din ya fita ya dauraye ya fito alokacin har bacci yakara daukan Yusrah akan sallaya,waje ya fita dan yaje ya shanya zanin gadon,abayan gidan da aka daura igiyar shanya,tasleem da tinda ta idar da sallah taji gabadaya dakinta yamata zafi,Palo ta fito,still jitayi yamata zafi,bude kofar ta tayi ta sauka kasa tayi bayan gida,tasamu guri ta zauna akan wani dakali dke kusa da inda aka shuka fulawowi,ta lumshe ido tanajin dadin iskan dake kadawa,cak el Bahrain ya tsaya daya hango tasleem azaune,ganin dayayi idanta alumshe ne yasa yayi sauri yaje ya shanya bedsheet din yadawo ya tsuguna agabanta,heart beat bude idanta tayi tasaukesu akan bed sheet din daya shanya dan tindaga tsayuwarsa har zua shanyar dayayi tana kallonsa,dawo da kallanta tayi kansa,aranta kuma tana mamakin yanda akayi sai yau ya kusance Yusrah duk tsawon lokacin nan,shikuwa ji yayi baiji dadin kara haduwarsu ba,dan ko bedsheet din data gani zai sa tagane,dakewa tayi tace ya jikin yusrah,dan sauki,heart beat ko zaki shiga kitchen ki samawa Yusrah Abu taci inkaita asibiti,dan har yanzu kanta ciwo yake,Kk babu matsala bari naje na Dora mana breakfast, ta Mike shima ya Mike,tayi bangarenta,yabi bayanta da kallo har ta shige,jiyayi ta bashi tausayi duk da tasan mai yafaru bata nuna kishinta ba.
Bangaren Yusrah ya shiga yaje ya tarar da ita a inda yabarta akwance deserved one yaringa tashinta ahankali ta bude idanta ta saukeshi akansa,nasa tasleem ta dafa mana abinda zamuci in kinci sai mutafi asibiti,yaya nifa na warke,zan Iya girki dakaina basai ka wahalar da Aunty tasleem ba,banyarda ba,Allah yaya gabobina ne kawai ke ciwo,eyya sorry dear hau gado inmiki tausa,zatayi magana yace shhhhh,bansan musu tashi tayi ta hau kan gadon ta kwanta ya tashi ya fara mata tausan ahankali,tasleem kua tana shiga bangarenta dakinta ta shiga taci kuka ta koshi,ta futo tashiga kitchen ta girka Abu mai saukin dahuwa ta juye a flask,ta ajiye akan dining tashiga bandaki tayi wanka tashirya da wani Riga da skirt pink da fari,hoda kawai ta Shafa ta fesa turare,karamin mayafi ta yafa fari,ta fito ta dauki tray din data Dora abincin ta sauka kasa ta nufi palon Yusrah gabanta na faduwa,el Bahrain kua tinda yafara yiwa Yusrah tausa wani bacci mai dadi yayi awon gaba da ita sabida dadin tausan datakeji,yana ganin tayi bacci ya tafi bandaki yayi wanka yazo ya shirya cikin kananan kaya ya fesa turare ya nufi Palo ya kunna TV yakamo tashar Al Jazeera yafara kallo,sallama tasleem tayi cikin sirriyar murya ya dago da sauri ya amsa,tare da mikewa ya karbi tray din hanunta ya ajiye yana mata sannu,sunkuyar dakanta tayi ta gaisheshi tare da tambayar mai jiki,matso wa yayi dab da ita ya rungumeta yana amsawa,tureshi tayi tana tambayar inda Yusrah take,yace mata bacci takeyi,amma Bari naje na tasheta,aa ka barta mana tayi baccinta watakila kafin ta farka zataji saukin ciwon kan,Bari inkoma dakina inta tashi na dawo,tace tajuya zata tafi, saurin ruko hanunta yayi to kibari muyi hira mana,kokarin kwace hanunta take Yusrah ta bude kofar dakinta ta fito,cika hanun tasleem yayi yanufi wajen Yusrah,deserved one kin tashi? Ya jikin naki? Yace yana ruko hanunta,zame hanunta tayi tace yaya naji sauki,Aunty tasleem ina kwana,tasleem da tunda el Bahrain ya cika mata hannu yayi wajen Yusrah jiki na rawa taji kirjinta na bugawa,jin yakirata da deserved one ne yasa kirjinta kara bugawa da karfi,dakewa tayi tace lafiya lau ya jikin naki,sauri tayi ta kalli el Bahrain sanan ta Ce dasauki dan tana tunanin ko yagayawa tasleem abinda yafaru ne,Allah yakara sauki,Ameen aunty tasleem,ga breakfast nayo mana kizo muci,sai kutafi asibiti,aunty naji sauki fa bakuma najin yunwa anjima zanci, aikuwa baki isa ba,el Bahrain yace yadauko train din abinci yazo ya ajiye atsakiyar carpet yaruko hanun Yusrah ya zaunar da ita,ya zauna agefenta,heart beat zauna ki zuba mana muci dan inkika biyewa Yusrah baci zatayi ba,tasleem kua jikinta ne yaringa rawa tsigr jikinta yatashi sabida kishi,azuciyarta taringa karanta duk adduar dayazo bakinta,ta zauna tafara bude kulolin tana zuba abincin,Yusrah kua kicin kicin kwace hanunta take dan tana kunyar tasleem, bismillanku tasleem tace da rawar murya,Yusrah kua langwabewa tayi,el Bahrain yace au bazaki ci ba,bari kiga nabaki dakaina,ya debo abincin yanufi bakin Yusrah kau dakanta tayi ya,janyota tafada jikinsa yarike fuskarta oya haa in baki,to yaya kacikani inci dakaina aa banyarda ba ki bude bakinki inbaki kinsan bana san gardama ko,bude bakinta tayi ya zuba mata,tasleem kua jikinta ne yaringa rawa sosai,har cokalin hanunta,kai cokalin sa dayayi dan yakara debowa yaga hanun tasleem nata rawa,Daga idansa yayi ya kalleta yaga kamar hawaye ke zubo mata.Ajiye cokalin hanunsa yayi dan wani mugun tausayin tasleem ne ya rufeshi sai yanzu yake ganin bai kyauta mata ba,ajiye cokalin hanunsa yayi,yace Yusrah cigaba da cin abincinki,tasleem kua ganin inta kara minti daya agurin ba abinda zai sa kukan daya taho mata yakwace mata yasa ta ajiye cokalin tayi hanyar waje,heart beat,el Bahrain yace yana mikewa,kafin ta karasa kofa,izzadeen yafado palon kamar Wanda aka jefo dan saura kiris suyi gware da tasleem,ja da baya tayi dasauri,shikuma izzadeen mutuwar tsaye yayi ya zuba mata ido,dan ganin wani kyau da tasleem takarayi ga shigar datayi yasa ya hadiyi yawu ba shiri, cikin zafin nama el Bahrain ya finciko tasleem yamaida ta bayansa ya watsawa izzadeen wani mugun kallo kai wane irin dabanci ne wanan zaka shigo gidan mutane babu sallama,yi hakuri abokina wlh ba a nutse nake bane shiyasa namanta banyi sallama ba,juyawa yayi ya kalli tasleem data makale abayansa yace wuce kitafi dakina,jiki na rawa tayi hanyar dakin el Bahrain da dan gudunta,izzadeen kua ya hau Daga wuya dan yaganta,Yusrah koma dakinki xamuyi magana da izzadeen kwashe kayan abincin,ki tafi dakina kuci abincin,Yusrah ta Mike ta gaida izzadeen ya amsa,tadauki farantin tayi hanyar dakin el Bahrain,sai dayaga ta shige yadawo da kallonsa kan izzadeen ya nuna shi da yatsa,izzadeen this should be the first and last time daxaka shigo min gida ba sallama,dan wlh ka karayi sai namaka mugun rashin mutunci,akan me xaka fado min gida ahaka,haba kamal nabka hakuri ai mai na mita kuma wlh ba a nutse nake bane shiyasa,lafiya mai kazo nema agidana dasassafen nan ba jiya aka kaima Amarya ba,kara tamke fuskarsa yayi yace abinda yakawoni kenan dan tun jiya nake gwada layinka akashe,kamal suhaima ta cuceni wlh sai na saketa bazan zauna da ita ba,waro ido el Bahrain yayi yana kallonsa yataba kan izzadeen da alama dai kalau kake,ballantana ince ko bakasan mai kake cewa ba,sweet pie dinka sweet 16 dinka zaka saka mai yayi zafi haka,haba kamal ina gaya maka zancen serious kana min wani zancen banza,to kafadamin mai tayi maka mana,could u believe suhaima ba virgin bace,hasali ma yanda kasan kofar taxi haka take,kwanciya el Bahrain yayi yafara kyalkyale dariya😂😂 yana rike ciki,wani irin bakin ciki ne yarufe izzadeen, wanan wane irin wulakancine inzo ingaya maka magna ka hau yimin dariya,me abun dariya nan😡,😡mikewa el Bahrain yayi still yana dafe da cikinsa,izzadeen idan banyi dariya ba kuka kakeso nayi,abinda ka shuka shi kafara girba tun yanzu,ko bansha gaya maka ka daina L🅰L🅰T🅰 yayan mutane ba,suma wayanda ka lalata zasuyi aure, exactly abinda kaji yanzu suma haka mazajensu zasuji,sabida haka hakkin yayan mutane ne yakamaks,oga sweet sixteen, wai kai mai wayyo ka gama lalata yayan mutane kasamu er sweet sixteen ka aura,ina abokina ai fasiki sai fasika,Allah ne yanuna maka ishara Tun agidan duniya, sai ka fara istigifari tin yanzu Allah ya tsayar a Iya kan suhaima,tunda el Bahrain yafara magana izzadeen yaji ransa nakuma baci,naji ustaz,inaga dai duk wayanda na lalata su sukawo kafarsu wajena ban bisu har gidan iyayensu ba,ciki kua harda matarka tasleem,ee itama kaddara ne ya afka mata amma matata nagartaciya Ce,dan dama haka Allah ya hukunta sai yafaru,dan ba irin taka bace data gama bin maza harta zama kofar taxi, wani irin bacin rai ne yakara rufe izzadeen bakomai kamal ni nataka nazo inda kake har kake gayamin magana suhaima ai ba dole bane inzauna da ita ba sakinta zanyi in auro wata, kanka akeji, dan ko dubu zaka aura lallataciya zaka aura dan baka isa kayiwa Allah wayyo ba.

YOU ARE READING
LALATA
RomanceLabarin Tasleem data had'u da mayaudari har ya rabata da martabarta ta diya mace a karshe ya juya mata baya