*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*
_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_
*Intelligent Writers Association*✏
*Srry 4d late update...Bohot bohot love Habibaties...*
*Chapter 12*
_Kaduna_
"""Yau din Takama weeked ne,Lahadin karshen mako ne,kowani soja dake barikin manya da kanana suna gidajensu domin Hutawa hakane ta faru da Captain Aliyu,Shima din Tunda ya dawo sallar asuba yakoma bai iya tashi ba saboda gajiya da barci.
Cikin barci yakejin kiran waya da karan Door bell atare,Wayar nasa tana kan Side Drower din gadon nasa ne,hannu kawai ya mika ya dauko wayar da niyyar kasheta sunan Jabir daya gani ne,yasashi ya daga kiran yana fadin",Hey Dude wht wrong kakemin irin wannan kiran..? ya fada Muryansa da alamun barci daga chan bangaren Jabir ya amsa da fadin"Dallah mallah ka watsake daga wannan barcin Gani akofar Apartment dinka.."Aliyu najin haka ya datse kiran yana tsaki yasan halin Jabir kamar maye da takura,mirginawa yayi gefe ya cigaba da barcinsa ammh sai me karan Door bell din fa bai tsaya ba,har filo yasa ya Toshe kansa ammh duk abanza,Mikewa yayi ya duro daga kan gadon,sanye yake da wani 3quater din wando babu ko Riga ajikinsa ya fito daga bedroom din yana bata rai isa yayi isa ga kofar ya bude jabir dake Tsaye hannu harde akirji Ya bayyana Kare kofar Aliyu yayi yana rollin din idonsa kafin yace"Ya? lafiya mallam kazo kahanani barci sai famam bugamin kofa kake sai kace naci bashinka ban biya ba.."?ya fada yana ballamasa harara.
Yar dariya Jabir yayi kafin yace"Ba laifina bane Captain,banbin ka bashi ammh akwai mai binka.."Yafada yana shafa sajen Fuskarsa,Shekeke Aliyu ya kallesa kafin yace"Toh waye..? Jabir yayi Saurin matsawa baya sai ga Ni"ima ta bayyana tana sanye da Doguwar riga Baka kirar Armani,tayane kanta da bakin mayafi,kafarta sanye da wani black halfcover,mai kyau da tsari,sai wata karamar jaka,da wayarta dake hannunta,Sake baki Aliyu yayi yana bin Ni"ima da kallo daga sama har kasa,itako Tunda ya fito take kallonsa gabadaya wani soyayyarshi data binne lungu da sako Ya tasomata lokaci daya hawaye suka cikamata ido saboda tsausayin kanta.
Rausayar dakai Jabir yayi kafin yace"Toh na fita ko? Kai mallam ka bata hanya Ta shiga ciki takanas daga gombe take saboda kai,ko bakomai ka girmama bakonka.."Jabir na fadin haka ya wuce ya barsu nan,Ni'ima dake tsaye batayi gaba batayi baya ba,kallonsa kawai take hawaye suka gangaromata baki na Rawa ta Furta.."Soja..Nah...",Tafada cikin muryan kuka kafin tatafi da gudu ta fada jikinsa sai kuma ta saki kukan lokaci daya,Ajiyar zuciya Captain ya sauke kafin yayi baya bayan ya sanya kafa ya Rufe kofar takoma Tarufe kanta,hannu ya sanya yana buga bayan Ni"ima lallashi itako Fadi take"Why my Captain? why..? .meyasa zaka barni alokacin danake tsananin bukatarka da burin na sameka? wlh koda da darana daya bantaba samun kwanciyar hankali da barci mai dadi ba Tunda na Rasaka don Allah Sojana kada ka sake gujemin wlh bazan iya Rayuwa baka ba,nasha wahala kafin na sameka...",Tafada tana kara kamkameshi,tanasakin wani marayan kuka.
Bambareta yayi daga jikinsa ya isa da ita kan daya daga cikin kujerun Falon ya zaunar da ita,Kichen Ya nufa yaje ya daukomata Ruwa da wani karaminn kofi ya Tsiyayamata mikamata yayi yana kallon kwanyan Idonta,Amsa tayi kafin ta sanya hannu ta share hawayenta,dan kurba tayi kadan kafin ta mikamai,kan Center table din dake Falon ya ijiye kofin kafin ya koma kujeran dake kallon nata ya zauna bayan Ya Dora kafa daya kan Daya yana Fuskarta dago da kanta tayi Tana kallonsa Shiko Remot ya dauka yana sarrafa talabijin din dake Falon.
"Soja...Nah...."Tafada cikin Rawan murya Dagowa yayi zata kara mgana yayi Saurin dagamata hannu yana fadin",Kinga nifa bani zakizo kina ma kuka ba,babanki zaki tasa kikatayima Kuka domin shi yasaka alkamashi ya datse halakan dake tsakani na dake..."Ya fada idonsa akanta Raurau tayi da ido kafin tace", i know buh..."Dagamata hannu yayi kafin ya mike yana fadin",Ki Adana kalamanki Ni"ima domin basu da muhalli awajena,Ba shakka ada na soki,na kuma so muyi,zama na har abada dake,sai dai kash Tun Ranar da mahaifinki ya watsamin kasa a ido naji kin Fita Raina,ko koda ace banyi Aure ba bazan Taba iya Aurenki ba,..."Yafada kai tsaye
