P 1

187 4 0
                                    

*WATA UNGUWA*

*(Labari game da wata hargitsattsiyar unguwa mai cike da abubuwan mamaki da al'ajabi)*

Alƙalamin: RUƘAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)

Marubuciyar: SOYAYYAR MEERAH.
*YAR GANTALI*
*RIKICIN MASOYA*
*A SANADIN KAMA*
*RASHIN GATA(GAJEREN LABARI)*
*HALITTAR ALLAH CE*

AND NOW
*WATA UNGUWA*

GODIYA: Dukkan godiya ta tabbata ga Allah maɗaukakin sarki buwayi gagara misali Sarkin da ya aramun rayuwa da lafiya ya kuma bani basira da damar rubuta wannan littafi domin ya zama faɗakarwa da jan hankali a rayuwa al'umma baki ɗaya.

Tsira da aminci su ƙara tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam
Tare da iyalan gidansa da sahabbansa baki ɗaya.

*Gargadi:* Ban yarda wata ko wani ya canza mun labari ta kowacce siga ba ba tare da izinina ba.

Wannan labarin ƙirkirarren labari ne ban yi hi domin cin zarafin wani ko wata ba wanda hakan ya yi daidai da rayuwarsa to aradhi ne kawai.

*AREWA WRITERS ASSOCIATION*

*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*

Free page
P 1

BABI NA ƊAYA

GARIN MAMBIYA
UNGUWAR GARWA

Da misalin ƙarfe 6 na safiyar ranar Lahadi unguwar ta yi tsit baka jin motsin komai sai na iskar dake kaɗawa, titin ya yi tsit kamar ba wani mahaluƙi dake rayuwa kusa da gurin.
Bayan shuɗewar mintuna biyu sai ga wata dalleliyar baƙar mota ta hawo titin da alama matuƘin motar ya na cikin hanzari ne. Can kuma motar ta ci burki dai-dai kan wani ƙaramin layi.

Daga cikin motar wata matashiyar budurwa ce da ba zata haura shekaru 20 ba zaune a mazaunin mai zaman banza, Juyawa ta yi ta kalli wani babban mutum dake zaune a mazaunin Direba ta ce "Ya Alhaj ni zan ƙarasa gida ka san halin mutanen unguwar nan, da na sake wani ya ganni shi ke nan na shiga uku."

Yar dariya ya yi sannan ya kuma dubanta ya ce "Haba Hanee Baby daɗina dake masifar tsoro, don kin sha daɗinki a waje miye?"

Tamke fuska ta yi tare da ɗora hannu kan Mabudin ƙofar motar zata fita. Cikin zafin nama Alhaji Saminu ya riƙo hannunta yana Faɗar "Haba habah! Hanee Baby ki yi haƙuri na daina kawo jakarki na saka miki kuɗin hajarki."

Banza ta masa kamar bata ji ba ya ɗauki jakar dake kan cinyarta yana murmushi irin na yan bariki, ya ciro kuɗi daga gaban motarsa Bandir na yan ɗari biyar-biyar rafa ɗaya ya saka mata a jaka, ya miƙa mata jakar.
Karɓa ta yi ta fita daga motar ba tare da ta ce komai ba.
A zahirin gaskiya gangar jikinta ce kawai take a gurin amma ruhinta yana gun tunanin me zai je ya dawo idan wani ya gan ta.
Sanye take da baƙar abaya amma a cikin jikinta riga da wando ne ɗamammu wanda sai ka aje hankalinka sosai zaka lura da hakan.

Tana fitowa ta ji wani irin sanyi na ratsa gaɓoɓin jikinta ta yanda har yake shiga ƙasusuwan jikinta.
Waige-waige ta hau yi ganin ba kowa ya saka cikin hanzari ta shige layinsu tana tafiya gudu-gudu sauri-sauri.

Abunda bata sani ba shi ne ashe tun lokacin da Alhajin ya faka mota Mamuda s/m yana zaune ketaren titin ya na kallonsu.
Tun lokacin da aka fito daga sallar asuba kowa ya koma gidansa ya rufe saboda tsananin sanyin da aka tashi da shi amma ban da Mamuda wanda ya Shimfiɗa ƙyalle ya zauna duk ya takure jikinsa saboda sanyi, amma baya son ya shiga gida don kada wani ya zo ya wuce ko ya yi wani abun bai gani ba tsabar munafunci.

Ya na ganin shigewar Hanifa layin ya miƙe tsaye ya na Faɗar "Kai! Ashe kura ce muke gani da fatar Akuya dama wannan yarinyar 'yar bariki ce? Ba mamaki...
Dariyar jin daɗi ya yi sannan ya koma ya zauna yana Faɗar "na samu rahoto na ɗaya bari na zauna ko a samu na tarawa."

WATA UNGUWAWhere stories live. Discover now