page 16

37 1 0
                                    

*WATA UNGUWA*
*(Labarin game da wata hargitsattsiyar unguwa mai cike da abubuwan al'ajabi)*

*ALƘALAMIN RUƘAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)*

*AREWA WRITERS ASSOCIATION*

*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*

10 Aug 2021

Page 16

BABI NA SHA SHIDA

DAWOWA DAGA LABARI

Bayan ficewar Baba Mudi daga gidan Inna ta koma kan tabarma ta zauna tana jin zogi a idonta a bayyane ta ce "Wannan wace irin Zuciya ce gare ka Mudi? Ji yanda kake neman makantar da ni, baya ga wannan ɗanyen aikin da ka yi kan ƴaƴana."

Su kuwa su Hanifa sai da suka tabbatar da ya bar gidan kafin su sake juna, kowa ta koma makwancinta sai kuka suke kaɗan-kaɗan.

Ba ma kamar Hanee da take jin wata iriyar azaba tun lokacin da ya shauɗa mata bulala a saitin inda aka mata ɗinki, Allah ma ya kare ɗinkin bai walwale ba ai da bata ma san yanzu a wane hali take ciki ba.

Inna ma tana can tana fama da kanta, bata sake ko leƙo su ba, balle ta ga halin da suke ciki, wannan fa shi ake kira haihuwar guzuma ɗa kwance uwa kwance.

Suna nan a hakan Mankas ya shigo gidan ya sha ya yi Mankas, sai layi yake kamar zai kifa.

Bari zancen sallama don har ya manta yanda ake yinta, a haka ya nufi ƙofar ɗakinsu Hanifa cikin Muryar maye yake faɗar "Ina wannan tantiriyar ɓoyen? ki fito ki ban wani abu yau ko na tona asirinki a cikin gidan nan." Yana maganar ne yana ƙara kusantar ɗakin.

Ras! Kirjin Hanee ya buga da ƙarfi a ranta ta ce 'Shike nan na shiga ɗari, ya je ya sha abunsa zai zo ya tonan asiri.' nan take ta nemi zogin ciwon da take ciki ta rasa, da ƙarfi ta yunƙura ta nufi ƙofar, tare da tarbe shi kafin ya ƙaraso ciki.

A dai-dai lokacin inna ke faɗar "Allah ya shirye ka Suleman! Yau ma abun ka shawo ko? Wa kake faɗar zaka tonawa asiri?." Ta yi maganar kamar mai shirin yin kuka.

Har ya buɗi baki zai yi magana Hanee ta yi saurin saka hannunta ta toshe masa baki, da yake Innar tana nesa da su a bayan katangar ɗakin take, saboda haka bata iya hangensu sai dai ta ji sautin.

"Ina jinka Suleman da wa kake magana?." Innar ta kuma faɗa.

A hankali Hanifa ta je saitin kunnansa ta raɗa masa wata maganar, sai ga murmushi ya bayyana a fuskarsa duk kuwa halin da yake ciki.

Daga can ya ɗago muryarsa da har yanzu bata sake ba ya ce "Gaskiya Inna kin cika sa ido, kina yawa fa."

Ai Inna na jin haka, ta wuce ɗakinta cikin hanzari, 'yar kwallar da ta taru a idonta tana neman shanyewa, sai ga shi ta zubo.

Tabbas kuwa dama 'yan magana sun ce 'duk abinda ka shuka shi zaka girba.' yau dai ga shi tana girbar sakamakon fanɗarewa da rashin girmama iyayenta da ta yi a baya.

A ƙasan yagaggiyar ledar ɗakin ta zauna tana tunanin baya.
A take majigin ƙwaƙwalwarta ya shiga hasko mata lokacin baya.

Watarana da misalin ƙarfe sha daya na dare ta shigo gidansu cikin hanzari, ta wuce makwancinta, abu kawai ta ɗauka cikin sauri, ta kama hanya za ta fita kenan, ta jiyo muryar Innarta daga bayanta "Luba ina kuma za ki? Duk yinin da kika yi a waje bai ishe ki ba, sai kin koma kin kwana?" Cikin damuwa Innar tata ke magana.

Da yake a lokacin ta riga ta fanɗare, wani uban tsaki ta ja tare da juyowa a fusace "Gaskiya Inna kina da matsala! Kin cika sa'ido, wannan fa rayuwata ce ba taki ba." Tana gama faɗa ta yi gaba abunta, ba ta ko damu da halin da Innar zata shiga ciki ba.

Has llegado al final de las partes publicadas.

⏰ Última actualización: Nov 25, 2021 ⏰

¡Añade esta historia a tu biblioteca para recibir notificaciones sobre nuevas partes!

WATA UNGUWADonde viven las historias. Descúbrelo ahora